Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi kakkausar suka kan barazana da sukar da ake yi wa Shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan, yana mai bayyana su a matsayin abin ƙyama da ke iya kawo cikas ga tafiyar dimokuraɗiyya a ƙasar.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Juma’a, Sanata Sani ya ce kai wa shugaban INEC hari ta hanyar barazana, ko rashin amincewa da shugabancinsa ko kuma zarge-zarge “ba shi ne hanya mafi dacewa ba,” musamman yayin da ake tunkarar babban zaɓen 2027.
- Sanata Shehu Sani Ya Buƙaci Al’ummar Kaduna Su Zaɓi Mutane Masu Mutunci A Zaɓen 2027
- Manzon Allah SAW Abin Kowa Ya Yi Murna Da Shi Ne
Maganarsa ta zo ne a daidai lokacin da Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC) da Majalisar Shari’ar Musuluncii ta Nijeriya suka yi kira ga Shugaba Bola Tinubu da ya gaggauta cire Amupitan daga muƙaminsa. A gefe guda kuma, Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) a Jihohin Arewa ta ja kunnen ƙungiyoyin addini da kada su bari a yi amfani da su wajen matsin lamba na siyasa.
CAN ta buƙaci Majalisar Shari’a da ta bayyana a fili ko duk wani mutum ko ƙungiya da ke bayan yaƙin neman a cire shugaban INEC, tana mai jaddada cewa dandamalin addini bai kamata ya zama “mafaka mai sauƙin amfani” ga muradun siyasa ba.
Da yake mayar da martani kan ce-ce-ku-cen, Shehu Sani ya jaddada muhimmancin kare cibiyoyin dimokuraɗiyya, yana mai cewa ya kamata a tallafa wa jagorancin INEC maimakon yi masa barazana, domin tabbatar da gudanar da sahihin zaɓe wanda shi ne ginshiƙin ci gaban dimokuraɗiyyar Nijeriya.















Discussion about this post