Jama’a barkanmu da juma’a, barkanmu da sake kasancewa tare da wannan shafi na GORON JUMA’A. Shafin dake bawa kowa damar mika sakon gaishe-gaishensa zuwa ga ‘yan’uwa da abokan arziki, na kusa da na nesa, har ma da wadanda aka dade ba a hadu ba.
Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wasu sakonnin gaishe-gaishen da kuka aiko mana kamar haka:
- Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
- Dambarwar Da Ta Biyo Bayan Sauya Sheƙar Gwamna Yusuf Na Jihar Kano
Sako daga Jafar Mu’azu, Kantagora:
Ina mika sakon goron juma’a zuwa ga, Lami me sakwara, da Hajiya Abu, da Hajiya Lauratu mai adashi, ina gaida yarinya ta Bintu, da Asabe da Mardiyya, Allah ya sa za su yi juma’a lafiya.
Sako daga Abdullahi Yahaya, Rijiyar Lemo Jihar Kano:
Sakon gaisuwa ta zuwa ga sahibata abar kaunata Zainab Kabir, da kuma kannenta Aisha da Maryama da kuma Auwal, ina gaida mahaifiyata Hadiza Isma’il da babana Alhaji Yahaya mai atamfa, ina gaida abokaina wadanda muke tare da su, da wadanda ba ma tare a yanzu ina gaishe su a duk inda suke, da fatan za su yi juma’a lafiya.
Sako daga Rahinatu Idris (‘Yar Mala), Jihar Kaduna:
Ina gaishe da kawayena kamar su; Hajara, Latifa, Maimuna, Baby ‘yar Mama, Sadiya Abdulrahman, Hauwa’u Abba, fiddausi da dai sauransu, ina yi musu addu’a su yi juma’a lafoya. Sannan ina gaida Ummana Hajiya Momi da Abbana Alhaji Idris da kuma kannena da yayyena, Allah ya hada mu da alkhairan ranar.\
Sako daga Safiya Ibrahim, Jihar Jos:
Ina gaishe da habibi mai sunan ‘yan gayu Nasir Bashir Ahmad, masoyina in sha Allah, ina gaida Antis di na Anti Farida, da Anti Maryam, da Anti Jamila, da Anti Ummi. Ina gaida kanwata rigimammiya ‘yar autan Momi Hafsat da sauran kannena, da fatan za su sha ruwa lafiya.
Sako daga Aliyu Salis, Jihar Kano:
Ina gaida al’ummar musulmi bakidaya na fadin duniya, ina kuma yi wa kowa addu’ar Allah ya kawo mana mafitar halin da ake ciki, ina kuma addu’a wannan rana da muke ciki Allah ya sa kowa yayi juma’a lafiya, ina gaishe da kowa na gidanmu tun daga kan mahaifana har zuwa kn yayyena da kannena da kuma abokanaina, Allah ya ba mu ladan wannan rana ta juma’a.














Discussion about this post