An haifi Magajin Gari Muhammadu Sambo a Zariya a shekara ta 1888 marigayi Magajin Gari Sambo shi ne wanda ya ƙirƙiri Kaduna ta zamani, bugu da ƙari kuma shi ne Malamin makarantar Boko na farko ɗan asalin Arewa,
Alaƙarsa da ilimi ta fara ne daga shekara ta 1903 a Makarantar Lardi ta Kano, inda ya ke shi ne ɗalibi na takwas da aka rubuta sunansa a rajista. Daga 1903 zuwa shekarar 1908, ya shimfiɗa tubalin sadaukar da rayuwarsa ga neman ilimi, wayewa, da kuma koyar da shi.
A shekarar 1910,ya zama Malami mai kulawa da sauran Malaman makaranta da yadda ake tafiyar da ita (Hedimasta) ɗan asalin ƙasa ɗan Arewa na farko a Makarantar Lardi ta Zariya (wadda a yanzu ake kira da suna Alhuddahudda College ko kuma Kwalejin Alhuddahudda). Nasarar da ya yi ta nuna irin jajircewar da yake da ita wajen ci gaban ilimi. A 1912, aka naɗa shi Hedimasta na farko a Makarantar midil ta Bauchi (wacce daga baya aka sani da sunan Kwalejin ilimi ta Sambo ).A can ne ya koyar da ilimi tare da ƙarfafa tunani mai zurfi da neman ilimi.
A shekarar 1916, sai aikinsa ya ɗauki sabon salo a lokacin da Sarkin Zazzau Aliyu Ɗan Sidi ya naɗa shi Wamban Zazzau kuma Hakimin Jaji. A wancan lokacin ya fara gina wani gidan baƙi (guest house) wanda daga baya ne ya zama Command and Staff College Jaji, wato babbar cibiyar horar da manyan Sojoji ta Nijeriya.
Sai dai a 1920, Sarkin Zazzau Dalhatu ya ƙwace masa Sarauta, amma hakan bai sa ya fid da rai ba.
A shekarar 1923, aka sake karrama shi a lokacin da aka zaɓe shi ya jagoranci ƙungiyar Turawan Birtaniya da suka gudanar da ƙirga mutane ta farko (ƙidaya) a Arewacin Nijeriya. Sakamakon haka ne, sai Sarkin Ingila, Sarki George, ya ba shi takardar nambar yabo (Certificate of Honor) a 1924.
A 1925, aka dawo da shi Sarautar Hakimci tare da ba shi muƙamin Sarautar Hakimi mai kula da Sabon Gari Zariya. Ya taka muhimmiyar rawa wajen gina Sabon Garin, na Zariya, inda ya kafa makarantar firamare, da kuma haifar da sabbin unguwanni irin su Muchia da Dogon Bauchi daga 1927 zuwa 1930.
An samu maku wannan ne daga Dandalin Tarihin Magabata za mu ci gaba a mako mai zuwa,















Discussion about this post