ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa (Hedimasta) (1)

by Idris Aliyu Daudawa
2 months ago

An haifi Magajin Gari Muhammadu Sambo a Zariya a shekara ta 1888  marigayi Magajin Gari Sambo shi ne wanda ya ƙirƙiri Kaduna ta zamani, bugu da ƙari kuma shi ne Malamin makarantar Boko na farko ɗan asalin Arewa,

Alaƙarsa da ilimi ta fara ne daga shekara ta 1903 a Makarantar Lardi ta Kano, inda ya ke shi ne ɗalibi na takwas da aka rubuta sunansa a rajista. Daga 1903 zuwa shekarar 1908, ya shimfiɗa tubalin sadaukar da rayuwarsa ga neman ilimi, wayewa, da kuma koyar da shi.

A shekarar 1910,ya zama Malami mai kulawa da sauran Malaman makaranta da yadda ake tafiyar da ita (Hedimasta) ɗan asalin ƙasa ɗan Arewa na farko a Makarantar  Lardi ta Zariya (wadda a yanzu ake kira da suna Alhuddahudda College ko kuma Kwalejin Alhuddahudda). Nasarar da ya yi ta nuna irin jajircewar da yake da ita wajen ci gaban ilimi. A 1912, aka naɗa shi Hedimasta na farko a Makarantar midil ta Bauchi (wacce daga baya aka sani da sunan Kwalejin ilimi ta Sambo ).A can ne ya koyar da ilimi tare da ƙarfafa tunani mai zurfi da neman ilimi.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1916, sai aikinsa ya ɗauki sabon salo a lokacin da Sarkin Zazzau Aliyu Ɗan Sidi ya naɗa shi Wamban Zazzau kuma Hakimin Jaji. A wancan lokacin ya fara gina wani gidan baƙi (guest house) wanda daga baya ne ya zama Command and Staff College Jaji, wato babbar cibiyar  horar da manyan  Sojoji ta Nijeriya.

Sai dai a 1920, Sarkin Zazzau Dalhatu ya ƙwace masa Sarauta, amma hakan bai sa ya fid da rai ba.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

A shekarar 1923, aka sake karrama shi a lokacin da aka zaɓe shi ya jagoranci ƙungiyar Turawan Birtaniya da suka gudanar da ƙirga mutane ta farko (ƙidaya) a Arewacin Nijeriya. Sakamakon haka ne, sai Sarkin Ingila, Sarki George, ya ba shi takardar nambar yabo (Certificate of Honor) a 1924.

A 1925, aka dawo da shi Sarautar Hakimci tare da ba shi  muƙamin Sarautar Hakimi mai kula da Sabon Gari Zariya. Ya taka muhimmiyar rawa wajen gina Sabon Garin, na Zariya, inda ya kafa makarantar firamare, da kuma haifar da sabbin unguwanni irin su Muchia da Dogon Bauchi daga 1927 zuwa 1930.

An samu maku wannan ne daga Dandalin Tarihin Magabata za mu ci gaba a mako mai zuwa,

Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta'adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.