ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa (Hedimasta) (1)

by Idris Aliyu Daudawa
1 month ago

An haifi Magajin Gari Muhammadu Sambo a Zariya a shekara ta 1888  marigayi Magajin Gari Sambo shi ne wanda ya ƙirƙiri Kaduna ta zamani, bugu da ƙari kuma shi ne Malamin makarantar Boko na farko ɗan asalin Arewa,

Alaƙarsa da ilimi ta fara ne daga shekara ta 1903 a Makarantar Lardi ta Kano, inda ya ke shi ne ɗalibi na takwas da aka rubuta sunansa a rajista. Daga 1903 zuwa shekarar 1908, ya shimfiɗa tubalin sadaukar da rayuwarsa ga neman ilimi, wayewa, da kuma koyar da shi.

A shekarar 1910,ya zama Malami mai kulawa da sauran Malaman makaranta da yadda ake tafiyar da ita (Hedimasta) ɗan asalin ƙasa ɗan Arewa na farko a Makarantar  Lardi ta Zariya (wadda a yanzu ake kira da suna Alhuddahudda College ko kuma Kwalejin Alhuddahudda). Nasarar da ya yi ta nuna irin jajircewar da yake da ita wajen ci gaban ilimi. A 1912, aka naɗa shi Hedimasta na farko a Makarantar midil ta Bauchi (wacce daga baya aka sani da sunan Kwalejin ilimi ta Sambo ).A can ne ya koyar da ilimi tare da ƙarfafa tunani mai zurfi da neman ilimi.

ADVERTISEMENT

A shekarar 1916, sai aikinsa ya ɗauki sabon salo a lokacin da Sarkin Zazzau Aliyu Ɗan Sidi ya naɗa shi Wamban Zazzau kuma Hakimin Jaji. A wancan lokacin ya fara gina wani gidan baƙi (guest house) wanda daga baya ne ya zama Command and Staff College Jaji, wato babbar cibiyar  horar da manyan  Sojoji ta Nijeriya.

Sai dai a 1920, Sarkin Zazzau Dalhatu ya ƙwace masa Sarauta, amma hakan bai sa ya fid da rai ba.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

A shekarar 1923, aka sake karrama shi a lokacin da aka zaɓe shi ya jagoranci ƙungiyar Turawan Birtaniya da suka gudanar da ƙirga mutane ta farko (ƙidaya) a Arewacin Nijeriya. Sakamakon haka ne, sai Sarkin Ingila, Sarki George, ya ba shi takardar nambar yabo (Certificate of Honor) a 1924.

A 1925, aka dawo da shi Sarautar Hakimci tare da ba shi  muƙamin Sarautar Hakimi mai kula da Sabon Gari Zariya. Ya taka muhimmiyar rawa wajen gina Sabon Garin, na Zariya, inda ya kafa makarantar firamare, da kuma haifar da sabbin unguwanni irin su Muchia da Dogon Bauchi daga 1927 zuwa 1930.

An samu maku wannan ne daga Dandalin Tarihin Magabata za mu ci gaba a mako mai zuwa,

Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta'adda, Sun Ƙwato Makamai Da Abubuwan Fashewa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.