A daidai lokacin da Jam’iyyar APC ke shirye-shiryen zaben fidda da gwani domin fuskantar babban zaven 2027, Sanata Abdulrahaman Buba Kwacham daya daga cikin masu neman Jam’iyyar ta tsayar dasu takarar kujerar Sanata a shiyyar Adamawa ta tsakiya ya yi watsi da shirin shugabannin Jam’iyyar na tsayar da Gwamnan Jihar Ahmadu Fintiri a matsayin dan takara da sunan ‘Sasanci’ wato ‘Concensors’.
Ya ce, wannan shiri babu hannunsa a ciki kuma ba da yawun al’ummar yankin aka yi ba. Sanata Abdulrahaman Buba Kwacham ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da manema labarai a gidansa da ke Abuja. Sanata Kwacham wanda kuma shi ne Sarkin Fulanin Mubi, ya yi gargadin cewa, wannan shiri ba zai haifa wa Jam’iyyar da mai ido ba, musamman a babban zabe da ke tafe. Ya kara da cewa, hanya daya tilo na warware wannan damnarwar ita ce na yin cikakken zaben fidda da gwani wato ‘Kato Bayan Kato’ ta haka hankalin duk wanda ya fadi zai kwanta za kuma a samu cikakken hadin kai a tsakanin ‘yan Jam’iyyar ta yadda za a tunkari babban zaben 2027 cikin tsari.
Ya kuma ce bai kamata Jam’iyyar ta yi irin kuskure da ta yi a lokuttan baya ba musamman a wasu jihohi inda ‘yan Jam’iyya suka koma gefe tare da yi wa Jam’iyyar zagon kasa.
Bayani ya nuna cewa, Gwamnan Jihar Ahmadu Fitiri ya sauya sheka ne daga jam’iyyar PDP zuwa APC inda kuma yake neman takarar kujerar Sanata tunda wa’adinsa na gwamna ya zo karshe.
Sai dai kuma burinsa na hawa kujerar ba tare da matsala ba yana neman samun cikas.















Discussion about this post