ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin “Gadar Abota Tsakanin Sin Da Najeriya” Zai Kara “Hada Zukatan Al’ummun Sin Da Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 month ago
Sin

Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da gidan rediyon muryar Najeriya (VON) sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a ran 18 ga watan nan da muke ciki, inda suka kaddamar da shirin koyar da harshen Sinanci mai suna “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” a hukumance. Wannan shiri mai minti 15 na koyar da harshen Sinanci da ake watsawa a kowane mako, ya aike da wani sako a fili cewa, hadin gwiwar Sin da Afirka yana tafiya daga “hadin gwiwar gina ababen more rayuwa” zuwa “hade zukatan al’ummun kasashen biyu”.

Najeriya ita ce babbar kasuwar samar da kwangilar ayyuka mafi girma ga Sin a Afirka, kuma ita ce kasa ta biyu mafi girma da Sin ke fitar da kayayyakinta. Daga layin dogo na cikin gari na birnin Abuja zuwa tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Lagos, daga gadar Oboroma zuwa layin dogo na Kano-Kaduna, ana bukatar dubban ma’aikatan Najeriya dake da kwarewar fasaha da kuma harshen Sinanci. Kwarewa a harshen Sinanci yana zama daya daga muhimman abubuwan da matasan Najeriya ke bukata wajen samun aikin yi.

Gidan rediyon na VON ne zai watsa shirin “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ga kasashen Afirka daban-daban, inda za a ba da labaran hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar koyar da harshen Sinanci, ta yadda karin al’ummar Afirka za su shiga cikin ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka. Babban daraktan VON Jibrin Ndace ya bayyana cewa, shirin zai samar da dandamali ga bangarorin biyu don kara fahimtar juna ta hanyar koyar da harshe da musayar al’adu.

ADVERTISEMENT

A hakika, ba wai mutanen Najeriya ne kadai suke son koyon Sinanci ba, har ma Sinawa da yawa a Najeriya suna kokarin koyon harsunan Najeriya, misali Hausa da sauransu. Mu yi tunanin lokacin da dan Najeriya ya ce “ni hao” da Sinanci, kuma ma’aikacin kamfanin Sin ya ce “na gode” da Hausa ko wani harshen kasar, to za a sami saukin tuntuba da zurfafa hadin gwiwa, kuma sakamakon hadin gwiwa zai amfanar da al’ummar wurin sosai.

Hadin gwiwar Sin da Afirka ba wai kawai yana dogara da kwarin gwiwar gwamnati da zuba jari na kamfanoni ba ne, yana kuma bukatar dinkewar zukatan jama’a. Da zarar an gina gadar harshe, kuma aka yi kyakkyawan dashen al’adu a tsakanin juna, za a gina wani dandamali mai karfi na musayar al’adu, kuma za a ci gajiyar cudanyar al’adu daga zuriya zuwa zuriya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

“Gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ba shiri ba ne kawai, har ma wata mahada ce, wanda ya shaida mana cewa, mataki na gaba da za a dauka na hadin gwiwar Sin da Afirka shi ne, a bai wa kowane dan Afirka damar cin gajiyar hadin gwiwar kasashen biyu, kuma ya rika ba da labarin abotar Sin da Afirka da bakinsa.

Wannan, shi ne ainihin matakin da ake dauka don tabbatar da ka’idar “tattaunawa a tsakanin juna da samun bunkasa da kuma more damammaki tare”.(Mai zane da rubutu: MINA)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.