Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da gidan rediyon muryar Najeriya (VON) sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a ran 18 ga watan nan da muke ciki, inda suka kaddamar da shirin koyar da harshen Sinanci mai suna “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” a hukumance. Wannan shiri mai minti 15 na koyar da harshen Sinanci da ake watsawa a kowane mako, ya aike da wani sako a fili cewa, hadin gwiwar Sin da Afirka yana tafiya daga “hadin gwiwar gina ababen more rayuwa” zuwa “hade zukatan al’ummun kasashen biyu”.
Najeriya ita ce babbar kasuwar samar da kwangilar ayyuka mafi girma ga Sin a Afirka, kuma ita ce kasa ta biyu mafi girma da Sin ke fitar da kayayyakinta. Daga layin dogo na cikin gari na birnin Abuja zuwa tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Lagos, daga gadar Oboroma zuwa layin dogo na Kano-Kaduna, ana bukatar dubban ma’aikatan Najeriya dake da kwarewar fasaha da kuma harshen Sinanci. Kwarewa a harshen Sinanci yana zama daya daga muhimman abubuwan da matasan Najeriya ke bukata wajen samun aikin yi.
Gidan rediyon na VON ne zai watsa shirin “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ga kasashen Afirka daban-daban, inda za a ba da labaran hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar koyar da harshen Sinanci, ta yadda karin al’ummar Afirka za su shiga cikin ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka. Babban daraktan VON Jibrin Ndace ya bayyana cewa, shirin zai samar da dandamali ga bangarorin biyu don kara fahimtar juna ta hanyar koyar da harshe da musayar al’adu.
A hakika, ba wai mutanen Najeriya ne kadai suke son koyon Sinanci ba, har ma Sinawa da yawa a Najeriya suna kokarin koyon harsunan Najeriya, misali Hausa da sauransu. Mu yi tunanin lokacin da dan Najeriya ya ce “ni hao” da Sinanci, kuma ma’aikacin kamfanin Sin ya ce “na gode” da Hausa ko wani harshen kasar, to za a sami saukin tuntuba da zurfafa hadin gwiwa, kuma sakamakon hadin gwiwa zai amfanar da al’ummar wurin sosai.
Hadin gwiwar Sin da Afirka ba wai kawai yana dogara da kwarin gwiwar gwamnati da zuba jari na kamfanoni ba ne, yana kuma bukatar dinkewar zukatan jama’a. Da zarar an gina gadar harshe, kuma aka yi kyakkyawan dashen al’adu a tsakanin juna, za a gina wani dandamali mai karfi na musayar al’adu, kuma za a ci gajiyar cudanyar al’adu daga zuriya zuwa zuriya.
“Gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ba shiri ba ne kawai, har ma wata mahada ce, wanda ya shaida mana cewa, mataki na gaba da za a dauka na hadin gwiwar Sin da Afirka shi ne, a bai wa kowane dan Afirka damar cin gajiyar hadin gwiwar kasashen biyu, kuma ya rika ba da labarin abotar Sin da Afirka da bakinsa.
Wannan, shi ne ainihin matakin da ake dauka don tabbatar da ka’idar “tattaunawa a tsakanin juna da samun bunkasa da kuma more damammaki tare”.(Mai zane da rubutu: MINA)















Discussion about this post