ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin “Gadar Abota Tsakanin Sin Da Najeriya” Zai Kara “Hada Zukatan Al’ummun Sin Da Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 weeks ago
Sin

Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da gidan rediyon muryar Najeriya (VON) sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a ran 18 ga watan nan da muke ciki, inda suka kaddamar da shirin koyar da harshen Sinanci mai suna “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” a hukumance. Wannan shiri mai minti 15 na koyar da harshen Sinanci da ake watsawa a kowane mako, ya aike da wani sako a fili cewa, hadin gwiwar Sin da Afirka yana tafiya daga “hadin gwiwar gina ababen more rayuwa” zuwa “hade zukatan al’ummun kasashen biyu”.

Najeriya ita ce babbar kasuwar samar da kwangilar ayyuka mafi girma ga Sin a Afirka, kuma ita ce kasa ta biyu mafi girma da Sin ke fitar da kayayyakinta. Daga layin dogo na cikin gari na birnin Abuja zuwa tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Lagos, daga gadar Oboroma zuwa layin dogo na Kano-Kaduna, ana bukatar dubban ma’aikatan Najeriya dake da kwarewar fasaha da kuma harshen Sinanci. Kwarewa a harshen Sinanci yana zama daya daga muhimman abubuwan da matasan Najeriya ke bukata wajen samun aikin yi.

Gidan rediyon na VON ne zai watsa shirin “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ga kasashen Afirka daban-daban, inda za a ba da labaran hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar koyar da harshen Sinanci, ta yadda karin al’ummar Afirka za su shiga cikin ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka. Babban daraktan VON Jibrin Ndace ya bayyana cewa, shirin zai samar da dandamali ga bangarorin biyu don kara fahimtar juna ta hanyar koyar da harshe da musayar al’adu.

ADVERTISEMENT

A hakika, ba wai mutanen Najeriya ne kadai suke son koyon Sinanci ba, har ma Sinawa da yawa a Najeriya suna kokarin koyon harsunan Najeriya, misali Hausa da sauransu. Mu yi tunanin lokacin da dan Najeriya ya ce “ni hao” da Sinanci, kuma ma’aikacin kamfanin Sin ya ce “na gode” da Hausa ko wani harshen kasar, to za a sami saukin tuntuba da zurfafa hadin gwiwa, kuma sakamakon hadin gwiwa zai amfanar da al’ummar wurin sosai.

Hadin gwiwar Sin da Afirka ba wai kawai yana dogara da kwarin gwiwar gwamnati da zuba jari na kamfanoni ba ne, yana kuma bukatar dinkewar zukatan jama’a. Da zarar an gina gadar harshe, kuma aka yi kyakkyawan dashen al’adu a tsakanin juna, za a gina wani dandamali mai karfi na musayar al’adu, kuma za a ci gajiyar cudanyar al’adu daga zuriya zuwa zuriya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

“Gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ba shiri ba ne kawai, har ma wata mahada ce, wanda ya shaida mana cewa, mataki na gaba da za a dauka na hadin gwiwar Sin da Afirka shi ne, a bai wa kowane dan Afirka damar cin gajiyar hadin gwiwar kasashen biyu, kuma ya rika ba da labarin abotar Sin da Afirka da bakinsa.

Wannan, shi ne ainihin matakin da ake dauka don tabbatar da ka’idar “tattaunawa a tsakanin juna da samun bunkasa da kuma more damammaki tare”.(Mai zane da rubutu: MINA)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.