ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin “Gadar Abota Tsakanin Sin Da Najeriya” Zai Kara “Hada Zukatan Al’ummun Sin Da Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago
Sin

Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da gidan rediyon muryar Najeriya (VON) sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a ran 18 ga watan nan da muke ciki, inda suka kaddamar da shirin koyar da harshen Sinanci mai suna “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” a hukumance. Wannan shiri mai minti 15 na koyar da harshen Sinanci da ake watsawa a kowane mako, ya aike da wani sako a fili cewa, hadin gwiwar Sin da Afirka yana tafiya daga “hadin gwiwar gina ababen more rayuwa” zuwa “hade zukatan al’ummun kasashen biyu”.

Najeriya ita ce babbar kasuwar samar da kwangilar ayyuka mafi girma ga Sin a Afirka, kuma ita ce kasa ta biyu mafi girma da Sin ke fitar da kayayyakinta. Daga layin dogo na cikin gari na birnin Abuja zuwa tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki a Lagos, daga gadar Oboroma zuwa layin dogo na Kano-Kaduna, ana bukatar dubban ma’aikatan Najeriya dake da kwarewar fasaha da kuma harshen Sinanci. Kwarewa a harshen Sinanci yana zama daya daga muhimman abubuwan da matasan Najeriya ke bukata wajen samun aikin yi.

Gidan rediyon na VON ne zai watsa shirin “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ga kasashen Afirka daban-daban, inda za a ba da labaran hadin gwiwar Sin da Afirka, ta hanyar koyar da harshen Sinanci, ta yadda karin al’ummar Afirka za su shiga cikin ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka. Babban daraktan VON Jibrin Ndace ya bayyana cewa, shirin zai samar da dandamali ga bangarorin biyu don kara fahimtar juna ta hanyar koyar da harshe da musayar al’adu.

ADVERTISEMENT

A hakika, ba wai mutanen Najeriya ne kadai suke son koyon Sinanci ba, har ma Sinawa da yawa a Najeriya suna kokarin koyon harsunan Najeriya, misali Hausa da sauransu. Mu yi tunanin lokacin da dan Najeriya ya ce “ni hao” da Sinanci, kuma ma’aikacin kamfanin Sin ya ce “na gode” da Hausa ko wani harshen kasar, to za a sami saukin tuntuba da zurfafa hadin gwiwa, kuma sakamakon hadin gwiwa zai amfanar da al’ummar wurin sosai.

Hadin gwiwar Sin da Afirka ba wai kawai yana dogara da kwarin gwiwar gwamnati da zuba jari na kamfanoni ba ne, yana kuma bukatar dinkewar zukatan jama’a. Da zarar an gina gadar harshe, kuma aka yi kyakkyawan dashen al’adu a tsakanin juna, za a gina wani dandamali mai karfi na musayar al’adu, kuma za a ci gajiyar cudanyar al’adu daga zuriya zuwa zuriya.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

“Gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” ba shiri ba ne kawai, har ma wata mahada ce, wanda ya shaida mana cewa, mataki na gaba da za a dauka na hadin gwiwar Sin da Afirka shi ne, a bai wa kowane dan Afirka damar cin gajiyar hadin gwiwar kasashen biyu, kuma ya rika ba da labarin abotar Sin da Afirka da bakinsa.

Wannan, shi ne ainihin matakin da ake dauka don tabbatar da ka’idar “tattaunawa a tsakanin juna da samun bunkasa da kuma more damammaki tare”.(Mai zane da rubutu: MINA)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

Obi Ya Ziyarci Kwankwaso Bayan Tantance Shi A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.