ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Gwamnati Na Samar Da Mafi Karancin Albashi

by Leadership Hausa
2 years ago
Mafi Karancin Albashi

A kwanakin baya ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da kwamitin mutum 37 don duba lamarin samar da mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan, an ba kwamitin umarnin tabbatar da fitar da tsarin mafi karancin albashi tare da la’akari mastalolin da al’ummar Nijeriya kie fuskanta a bangaren tattalin arziki da sauransu. A ra’ayinmu wannan wani abu ne mai matukar muhimmanci, an kuma umarci ‘yan kwamitin su fito da mafi karancin albashin da zai samu karbuwa ga dukkan matakan gwamnati. An kuma nemi su yi nazari tare da fitar da dalilan da ya hana wasu jihohi aiwatar da mafi karancin albashin da aka aiwatar a baya.

In aka lura da wanann umarnin daga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu za a fahimci cewa, shugaban kasa ya damu da al’amarin matsin rayuwu da ya shafi ma’aikatan gwamnati ne kawai. Amma in aka lura za a iya fahintar cewa, wannan ba karamin kuskure ba ne, don ya kamata a ce an samar da wata mafita ga ma’aikata masu aiki a bangaren kamfanoni masu zaman kansu domin suma suna fuskantar matsin rayuwa da dukkan ‘yan Nijeriya ke fuskatanta.

  • Tsadar Rayuwa: Majalisar Wakilai Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Lalubo Mafita
  • Cire Tallafin Fetur: Ma’aikatan Jihar Jigawa Sun Ki Amincewa Da Karin Albashin Naira 10,000

Amma kuma a ra’ayinmu, ya kamata a fahinci cewa, ‘yan Nijetriya da suke aiki a kamfanoni masu zaman kansu suma suna fuskantar matsalolin tattalin arziki da tsadar rayuwar da ake ji a halin yanzu. Haka kuma wadanda ma basa wani aiki na gwamnati ko kuma ma masu zaman kansu suma suna fatan gwamnati ta sa su a lissafi ta yadda za su samu jin saukin tashin farashin kayayyaki da zai faru in an kara wa ma’aikata albashi.

ADVERTISEMENT

Zuwa yanzu, bangarorin da ya ke tattaunawa a kan mafi karancin albashin sun fara ayyana wasu manyan kudade da ba zai a iya aiwatarwa ba. A ra’ayinmu, maimakon a ayyana wani albashi masu yawa wanda ba za a iya aiwatarwa ba, daga kaarshe abin ya tsaya kawai a takardar ba tare da an iya aiwatarwa ba. ya kamata a samar da tsarin da zai samu karbuwa ga dukkan bangarori. Ya kuma kamata a cire dukkan abin da ya shafi siyasa da son rai wajen aiwatar da mafi karancin albashin, musamman ganin irin wahalar da al’umma ke fama da shi a wannan lokacin.

A sharhin da muka gabatar a baya mun nemi a kara wa ma’aikata albashi, albashin da zai dauki dawainiyar rayuwar ma’aikaci. Za kuma mu ci gaba da da’awar neman a a tabbatar da an kara wa ma’aikacin Nijeriya albashi. A bayyana yake cewa, duk irin kudin da aka biya mai karbar albashi ba zai taba isansa tafiyar da raywuarsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

A cikin sharhin da muka yi mun nemi gwamnati ta sa hannu a dukkan bangarorin rayuwar al’umma Nijeriya gaba daya ba wai na masu karbar albashi kawai ba, al’amarin ba kawai na albashi ba ne, harma na abin da albashin zai iya saya.

Wannan ne ya kawo mu a kan bukatar a gagguta sake fasalin albashi da tattalin arzikin kasa baki daya. Ta yadda za a samu saukin farashin kayan masarufi. Duk da cewa, babu yadda albashi zai iya biya wa ma’aikaci bukatarsa amma albashin ya zamana zai iya raka ma’aikaci zuwa wani mataki mai muhimmanci a duk wata.

A ra’ayinmu duk yawan albashin da za a ba ma’aikaci a karshen wata ba zai taba isarsa ba in har aka ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan masarufi.

Yana da muhimmanci mu jawo hankalin gwamnati a kan tsadar kudin sufuri wanda a halin yanzu gwamnati ta bari a hannun bangarori masu zaman kansu, wanda suke amfani na lallacewar hanyoyinmu da hauhawar farashin albarkatun man fetur wajen tsawwala farashin kudin mota. A yayin da babu tsarin sufuri na gwamnati, kudaden sufurin da ma’aikaci zai ci gaba da kashewa zai ci gaba da hauhawa a waasu lokutta ma ba zai iya biya ba saboda tsada, duk kuwa da yawan albashin da gwamnati za ta ba ma’aikaci.

A bangaren kiwon lafiya, ‘yan Nijeriya da ke aiki a bangaren gwamnati da ma’aikatu masu zaman kansu ba su da wani tsarin kula da lafiya da zai tabbatar da kula da lafiyarsu dana iyalansu. Asibitocin gamnati da ake da su suma suna gwa-gwa ne da asibitoci masu zaman kansu wajen tsada.

Haka kuma, a kullum sai ka ji gwamnati na bayanin wai muna da gibin gidaje fiye da miliyan 16 amma kuma har yanzu bamu ga abin da ta yi ba don magance lamarin. A bangaren ilimi kuma, kusan gwamnati ta saki makarantu a dukkan mataki ga hannun masu zaman kansu.

A bayyana yake cewa, harkokin kasuwanci na tafiya a kasar nan ne tamkar babu gwamnati, ‘yan kasuwa sun zama gwamnatin kansu ta hanyar samar wa kansu abubuwan tafiyar da harkokinsu kamar, hanyoyi, ruwa, wutar lantarki da sauransu. Gwamnati na tuna dasu ne kawai in lokacin karbar haraji ya yi amma ba wai a yi muusu ayyyukan da zai sa su ji dadin tafiyar da harkokin kasuwancinsu ba.

Wadanan ko-in-kular ke kara zama kalubale ga tattalin arziki, musamman shi ne ke karya darajar kudin da ake karba da sunan albashi. Dole a ba gwamnati shawarar mayar da hankali a kan daukar matakan tabbatar da tattalin arzkin kasa yana tafiya. A ra’ayinmu, in har ana bukatar a samu ma’aikatan gwamnati da za su bayar da gudumawarsu wajen gina kasa dole a samar da tsarin tattalin arzikin tare da yaki da hauhawar farashi in ba haka duk karin albashin da za a yi zai zama matakin karin wahala ne kawai ga ma’aikata da sauran al’ummar Nijeriya.

Mafi Karancin Albashi
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Goro

Goron Juma’a

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

Yadda Ake Faten Dankalin Turawa Da Kaza

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

Baya Ga “Sanyi Irin Na Sin”, Akwai Wasu Abubuwa Da Yawa Da Masu Yawon Bude Ido Na Turai Ke Sha’awa Kan Kasar

July 25, 2026
Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.