ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Ya Umarci A Samar Da Sabuwar Kwalejin ‘Yansanda A Kudancin Nijeriya

by Sani Anwar
4 weeks ago
Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin kafa harabar makarantar koyar da ‘yansanda ta kudancin Nijeriya a Abeokuta, Jihar Ogun.

Hakan, na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka raba wa manema labarai a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun mai bai wa Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa shawara ta musamman, kan harkokin yada labarai da sadarwa, Ikharo Attah.

A cewarsa, ministan ya ce; Shugaba Tinubu, ya ci gaba da jajircewa, wajen kawo sauyi da sauya fasalin ‘yansandan Nijeriya, ta fannin ilimi da hanyar inganta makarantar ‘yansanda da sauran cibiyoyin ‘yansanda a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Alausa ya bayyana haka ne, a lokacin da babban sifeton ‘yansanda (IGP), Tunji Disu, ya jagoranci magabacinsa na ‘yansandan, Kayode Egbetokun, da wasu manyan jami’an ‘yansanda zuwa ofishinsa, domin wani taro kan makarantar da nufin kafa harabarta ta yankin kudu.

Ministan ya yi nuni da cewa, ‘yansanda na yi wa kasa hidima sosai, don haka; ya kamata kowa ya ba shi kwarin guiwa, domin yin aiki tare da samun nasara gwargwadon karfinsa.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Wannan taro na ci gaba ne da ajandar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, na sake mayar da ‘yansanda, don gudanar da ayyukansu da inganta tsaro a fadin kasar nan.”

Attah ya kara da cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne a kan tsarin samar da ababen more rayuwa nan take da kuma tsare-tsare na zahiri na sabuwar harabar makarantar ‘yansanda da ke Erije, Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Haka kuma a wajen taron, Ministan ya umarci Hukumar Jami’o’in Nijeriya (NUC), da ta gaggauta gudanar da aikin tantance kayan aiki, inda ya bayyana cewa; Shugaban kasar, yana son a tashi harabar jami’ar tare da karbar dalibai na farko tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.

An tattauna batun kwalejojin ‘yansanda sama da 42 da ke fadin kasar nan da nufin mayar da su na zamani.

Ministan ya yi nuni da cewa, “ana ci gaba da tattaunawa da ‘yansanda kan bukatar amincewa da kusan biyar zuwa shida daga cikin wadancan bukatu, don yin kwasa-kwasan da suka dace da masana’antu da ‘yansanda ke bukatar kara karfinsu.

“Na gana da sufeto-janar na ‘yansanda da tsohon IG da dukkan manyan ma’aikatan, BIG na horarwa da kuma AIG na horarwa da kuma AIG na makarantar ‘yansandan.

Sun kammala tattaunawa kan yadda za a kafa harabar makarantar ‘yansanda ta kudu, sannan an tattauna gaba-daya manufofin da sauran abubuwan da ake bukata.

“Aiki na biyu na NUC, yana tafiya cikin sauri don tabbatar da albarkatun, saboda manufar shugaban kasa na kwasa-kwasan ita ce, jami’ar ta tashi a wannan shekara tare da karbar dalibai na farko a tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.”

Har ila yau, ministan ya kafa kwamitoci uku wadanda babban sakataren hukumar NUC da AIG da kuma kwalejin ‘yansanda za su jagoranta.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Abba Yusuf Ya Miƙa Fom A Matsayin Ɗan Takarar APC

Gwamnan Kano Abba Yusuf Ya Miƙa Fom A Matsayin Ɗan Takarar APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.