ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Ya Umarci A Samar Da Sabuwar Kwalejin ‘Yansanda A Kudancin Nijeriya

by Sani Anwar
1 month ago
Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin kafa harabar makarantar koyar da ‘yansanda ta kudancin Nijeriya a Abeokuta, Jihar Ogun.

Hakan, na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka raba wa manema labarai a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun mai bai wa Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa shawara ta musamman, kan harkokin yada labarai da sadarwa, Ikharo Attah.

A cewarsa, ministan ya ce; Shugaba Tinubu, ya ci gaba da jajircewa, wajen kawo sauyi da sauya fasalin ‘yansandan Nijeriya, ta fannin ilimi da hanyar inganta makarantar ‘yansanda da sauran cibiyoyin ‘yansanda a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Alausa ya bayyana haka ne, a lokacin da babban sifeton ‘yansanda (IGP), Tunji Disu, ya jagoranci magabacinsa na ‘yansandan, Kayode Egbetokun, da wasu manyan jami’an ‘yansanda zuwa ofishinsa, domin wani taro kan makarantar da nufin kafa harabarta ta yankin kudu.

Ministan ya yi nuni da cewa, ‘yansanda na yi wa kasa hidima sosai, don haka; ya kamata kowa ya ba shi kwarin guiwa, domin yin aiki tare da samun nasara gwargwadon karfinsa.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Wannan taro na ci gaba ne da ajandar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, na sake mayar da ‘yansanda, don gudanar da ayyukansu da inganta tsaro a fadin kasar nan.”

Attah ya kara da cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne a kan tsarin samar da ababen more rayuwa nan take da kuma tsare-tsare na zahiri na sabuwar harabar makarantar ‘yansanda da ke Erije, Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Haka kuma a wajen taron, Ministan ya umarci Hukumar Jami’o’in Nijeriya (NUC), da ta gaggauta gudanar da aikin tantance kayan aiki, inda ya bayyana cewa; Shugaban kasar, yana son a tashi harabar jami’ar tare da karbar dalibai na farko tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.

An tattauna batun kwalejojin ‘yansanda sama da 42 da ke fadin kasar nan da nufin mayar da su na zamani.

Ministan ya yi nuni da cewa, “ana ci gaba da tattaunawa da ‘yansanda kan bukatar amincewa da kusan biyar zuwa shida daga cikin wadancan bukatu, don yin kwasa-kwasan da suka dace da masana’antu da ‘yansanda ke bukatar kara karfinsu.

“Na gana da sufeto-janar na ‘yansanda da tsohon IG da dukkan manyan ma’aikatan, BIG na horarwa da kuma AIG na horarwa da kuma AIG na makarantar ‘yansandan.

Sun kammala tattaunawa kan yadda za a kafa harabar makarantar ‘yansanda ta kudu, sannan an tattauna gaba-daya manufofin da sauran abubuwan da ake bukata.

“Aiki na biyu na NUC, yana tafiya cikin sauri don tabbatar da albarkatun, saboda manufar shugaban kasa na kwasa-kwasan ita ce, jami’ar ta tashi a wannan shekara tare da karbar dalibai na farko a tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.”

Har ila yau, ministan ya kafa kwamitoci uku wadanda babban sakataren hukumar NUC da AIG da kuma kwalejin ‘yansanda za su jagoranta.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Gwamnan Kano Abba Yusuf Ya Miƙa Fom A Matsayin Ɗan Takarar APC

Gwamnan Kano Abba Yusuf Ya Miƙa Fom A Matsayin Ɗan Takarar APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.