Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin kafa harabar makarantar koyar da ‘yansanda ta kudancin Nijeriya a Abeokuta, Jihar Ogun.
Hakan, na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka raba wa manema labarai a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun mai bai wa Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa shawara ta musamman, kan harkokin yada labarai da sadarwa, Ikharo Attah.
A cewarsa, ministan ya ce; Shugaba Tinubu, ya ci gaba da jajircewa, wajen kawo sauyi da sauya fasalin ‘yansandan Nijeriya, ta fannin ilimi da hanyar inganta makarantar ‘yansanda da sauran cibiyoyin ‘yansanda a fadin kasar nan.
Alausa ya bayyana haka ne, a lokacin da babban sifeton ‘yansanda (IGP), Tunji Disu, ya jagoranci magabacinsa na ‘yansandan, Kayode Egbetokun, da wasu manyan jami’an ‘yansanda zuwa ofishinsa, domin wani taro kan makarantar da nufin kafa harabarta ta yankin kudu.
Ministan ya yi nuni da cewa, ‘yansanda na yi wa kasa hidima sosai, don haka; ya kamata kowa ya ba shi kwarin guiwa, domin yin aiki tare da samun nasara gwargwadon karfinsa.
“Wannan taro na ci gaba ne da ajandar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, na sake mayar da ‘yansanda, don gudanar da ayyukansu da inganta tsaro a fadin kasar nan.”
Attah ya kara da cewa, tattaunawar ta ta’allaka ne a kan tsarin samar da ababen more rayuwa nan take da kuma tsare-tsare na zahiri na sabuwar harabar makarantar ‘yansanda da ke Erije, Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.
Haka kuma a wajen taron, Ministan ya umarci Hukumar Jami’o’in Nijeriya (NUC), da ta gaggauta gudanar da aikin tantance kayan aiki, inda ya bayyana cewa; Shugaban kasar, yana son a tashi harabar jami’ar tare da karbar dalibai na farko tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.
An tattauna batun kwalejojin ‘yansanda sama da 42 da ke fadin kasar nan da nufin mayar da su na zamani.
Ministan ya yi nuni da cewa, “ana ci gaba da tattaunawa da ‘yansanda kan bukatar amincewa da kusan biyar zuwa shida daga cikin wadancan bukatu, don yin kwasa-kwasan da suka dace da masana’antu da ‘yansanda ke bukatar kara karfinsu.
“Na gana da sufeto-janar na ‘yansanda da tsohon IG da dukkan manyan ma’aikatan, BIG na horarwa da kuma AIG na horarwa da kuma AIG na makarantar ‘yansandan.
Sun kammala tattaunawa kan yadda za a kafa harabar makarantar ‘yansanda ta kudu, sannan an tattauna gaba-daya manufofin da sauran abubuwan da ake bukata.
“Aiki na biyu na NUC, yana tafiya cikin sauri don tabbatar da albarkatun, saboda manufar shugaban kasa na kwasa-kwasan ita ce, jami’ar ta tashi a wannan shekara tare da karbar dalibai na farko a tsakanin watan Satumba da Nuwamban 2026.”
Har ila yau, ministan ya kafa kwamitoci uku wadanda babban sakataren hukumar NUC da AIG da kuma kwalejin ‘yansanda za su jagoranta.















Discussion about this post