Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya (NFF), Ibrahim Gusau, da wasu mambobin kwamitin zartarwar hukumar sun yi murabus daga mukamansu, a daidai lokacin da hukumar ke fuskantar matsin lamba sakamakon rashin nasarar da tawagogin ƙasar suka samu a manyan wasannin ƙasa da ƙasa. Matsalar ta ƙara tsananta ne bayan Super Falcons ta kasa samun gurbin shiga gasar cin Kofin Duniya ta mata ta FIFA a karon farko cikin shekaru 30.
A baya-bayan nan, hukumomin tsaro a Nijeriya sun fara bincike kan zargin karkatar da maƙudan kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ta ware domin biyan alawus-alawus da sauran buƙatun tawagogin ƙwallon ƙafa. Binciken ya shafi kudin da ya kai kusan Naira biliyan 17, inda Hukumar DSS da sauran hukumomin tsaro suka gudanar da bincike kan yadda aka tafiyar da kudaden a ƙarƙashin jagorancin Gusau.
Kwamitin zartarwar NFF ya fuskanci matsin lamba mai tsanani a ‘yan kwanakin nan, lamarin da ake ganin ya taka rawa wajen saukar wasu daga cikin manyan jami’an hukumar. Rahotanni sun ce mambobi takwas daga cikin 13 na kwamitin zartarwar NFF sun riga sun yi murabus, abin da ya kara haifar da tambayoyi kan makomar shugabancin hukumar.
Murabus din Gusau da sauran jami’an na iya shafar zaɓen shugabannin NFF da aka tsara gudanarwa a ranar 27 ga Satumba, 2026, a birnin Lafia na Jihar Nasarawa. Ana sa ran sabbin matakai za su biyo bayan murabus din, musamman ganin yadda hukumar ke fuskantar matsalolin gudanarwa da kuma bukatar sake farfaɗo da martabar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya.














