Rukunin farko na maniyyatan Jihar Sokoto domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 sun tashi daga Filin Jirgin Sama na Sultan Abubakar III da ke Sokoto a safiyar ranar Litinin.
Jirgin saman, na kamfanin UMZA Airline ya tashi da misalin ƙarfe 6:21 na safe dauke da alhazai 484 zuwa Filin Jirgin Sama na Prince Mohammad Bin Abdulaziz da ke Madina a ƙasar Saudiyya.
Alhazan sun ƙunshi maza 304 da mata 180 daga ƙananan hukumomin Tambuwal, Tureta, Wamakko, Sabon Birni, Isa, Shagari da Dange/Shuni na jihar.
Da yake jawabi kafin tashin jirgin, Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmad Aliyu Sokoto, wanda mataimakinsa Idris Muhammad Gobir ya wakilta, ya ce gwamnatin jihar ta ɗauki matakai masu kyau domin tabbatar da jin daɗi da tsaron alhazan a yayin sauke faralin.
Ya buƙaci alhazan da su zama jakadu nagari na jihar, yana mai jaddada cewa al’ummar Sokoto an san su da ladabi, zaman lafiya da kuma girmama hukuma.















Discussion about this post