Kwanan baya, rukunin jiragen ruwa masu dauke da jiragen saman yaki dake karkashin jirgin ruwan dakon jiragen saman yaki na Liaoning na rundunar sojin ruwan Sin, sun gudanar da atisaye na yau da kullun a cikin ruwan dake gabashin mashigar Miyako, atisayen da aka bayar da sanarwar aiwatarwa tun kafin lokacin. Sai dai a wannan lokaci, jiragen saman sojojin Japan sun yi ta kai ziyara yankin da sojojin ruwan Sin ke atisayen don cin zarafinsu, lamarin da ya yi mummunan tasiri ga horo na yau da kullum na jiragen saman yaki na Sin, da sanya tsaronsu cikin hadari.
Game da batun, mai magana da yawun rundunar sojin ruwa ta kasar Sin, babban kanar Wang Xuemeng ya bayyana cewa, kalaman da bangaren Japan ya furta game da batun, sun saba da gaskiyar lamarin. Ya ce suna kira ga Japan ta dakatar da bata wa Sin suna nan take tare da gyara matakan da take dauka. Yana mai cewa, rundunar sojin ruwan Sin za ta dauki matakan da suka dace bisa doka don kare tsaronta da hakkoki da muradunta.
Kakakin ma’aikatar tsaron Sin Zhang Xiaogang shi ma ya yi tsokaci kan lamarin, yana mai cewa, Japan ta ci gaba da cin zarafi a fannin soja, kuma kowa ya san ainihin manufarta. Idan Japan ta sake komawa ga ra’ayin nuna karfin soja, to babu mafita sai fada wa cikin wani mummunan yanayi.(Safiyah Ma)














