Dakarun Sojin Nijeriya da ke ƙarƙashin “Operation Whirl Punch” da “Operation Hadarin Daji” sun samu gagarumar nasara ta hanyar ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su, tare da daƙile yunƙurin hare-haren ‘yan ta’adda a jihohin Kaduna da Zamfara.
Sanarwar da shalƙwatar tsaro ta fitar ta nuna cewa jami’an sun yi amfani da dabarun yaƙi na zamani da kuma sahihan bayanan sirri wajen tarwatsa shirin ɓata-gari a yankunan.
A jihar Kaduna, dakarun Sojin sun yi nasarar ceto mutane guda tara da aka sace bayan sun fafata ƙazamin faɗa da ‘yan bindiga a kan babban titin Kaduna zuwa Abuja. Jami’an tsaron sun tilasta wa ‘yan bindigar tserewa zuwa cikin daji da raunukan harbin bindiga, inda sojojin suka ƙwato makamai da harsashi masu yawa daga maharan, gami da motocin mazauna yankin da aka yi yunƙurin sacewa.
Haka kuma a jihar Zamfara, Sojojin sun daƙile wani gagarumin hari da ‘yan ta’adda suka shirya kai wa a wata al’umma da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe. Dakarun sun yi wa ‘yan bindigar ƙwantan ɓauna kafin su ƙarasa cikin garin, inda suka kashe da dama daga cikinsu tare da tilasta wa sauran tserewa cikin daji; wannan mataki ya ceci rayukan ɗaruruwan mazauna yankin da dukiyoyinsu daga farmaki.
Babban kwamandan dakarun ya yaba da bajinta da juriya da jami’an sojin suka nuna a waɗannan fafatawa, inda ya jaddada aniyar rundunar na kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma.
Ya kuma yi kira ga mazauna yankunan da su ci gaba da ba wa dakarun tsaro haɗin gwuiwa ta hanyar kai rahoton duk wani motsi na shakku ko mutanen da ke ɗauke da raunin harbi a asibitoci.














Discussion about this post