Sojojin Rundunar Haɗin Gwiwa ta Yankin Arewa maso Gabas, Operation HAƊIN KAI (OPHK), sun samu manyan nasarori ciki har da daƙile wani harin ‘yan ta’adda, kama waɗanda ake zargi da taimaka musu, da kuma ceto wasu da aka sace.
A wani aiki da suka gudanar a Gajibo, sojoji sun daƙile harin da ake zargin mayaƙan Boko Haram/ISWAP suka shirya, inda suka taso daga ɓangarori daban-daban a kan babura.
Sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa, wanda ya tilasta wa ‘yan ta’addan ja da baya.
An kuma gano harsasai da wasu kayan yaƙi, kuma babu sojan da ya samu rauni.
A Gubio kuma, sojoji tare da taimakon Civilian JTF sun kama mutane biyu da ake zargi da taimaka wa ‘yan ta’adda.
A Gwoza, an kama wani mutum da ake zargin yana kai wa ‘yan ta’adda kayan abinci bayan samun bayanan sirri daga wani da ya miƙa kansa.
Haka kuma, wani yaro mai shekaru 17 da ke da alaƙa da ‘yan ta’adda ya tsere daga maɓoyarsu a tsaunukan Mandara ya kuma miƙa kansa ga sojoji, inda ya ce matsin lamba da ƙarancin abinci ne suka sa ya gudu.
Sojoji kuma sun ceto wasu maza biyu da aka sace a garin Mafa.
Sun tsere daga hannun masu garkuwa da su kuma yanzu suna samun kulawar lafiya.
Rundunar sojojin ta ce waɗannan nasarori na nuna yadda ake ci gaba da matsa wa ‘yan ta’adda lamba tare da lalata musu hanyoyin samun tallafi.
Ta kuma tabbatar da ƙudirinta na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.















Discussion about this post