ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan Boko Haram, Abu Khalid, Da Wasu 10 A Borno

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Sojoji

Sojojin rundunar Operation Haɗin Kai (OPHK) sun hallaka wani babban kwamandan Boko Haram mai suna Abu Khalid tare da wasu ƴan ta’adda 10 a dajin Sambisa, Jihar Borno. Lamarin ya faru ne kwana guda bayan da sojojin sashi na 1 tare da ‘yan CJTF suka hallaka Julaibib, wani kwamandan Boko Haram/ISWAP da ke aiki a yankin Gujba na Timbuktu Triangle.

A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na OPHK, Laftanar Kanal Sani Uba, ya fitar, ya ce an samu nasarar ne a daren Asabar bayan sojoji sun yi artabu da ƴan ta’adda a yankin Komala, Ƙaramar Hukumar Konduga ta Jihar Borno, da misalin ƙarfe 11 na dare.

  • Sojoji Sun Kama Tsohuwa Mai Shekaru 65 Bisa Zargin Safarar Ƙwayoyi Ga Ƴan Boko Haram
  • Boko Haram Sun Kai Hari Sansanin Sojoji A Borno

Uba ya bayyana cewa Abu Khalid ya kasance muhimmin jigo a tsarin Boko Haram, yana da alhakin shirya ayyuka da kula da kayan aiki a yankin Sambisa. Bayan artabun, sojoji sun ƙwato bindigogi AK-47 guda biyar, da sinƙin harsashi, da kekuna, da kayayyakin abinci da na magani masu yawa.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa babu wani rauni ko asara a ɓangaren sojoji, inda ya jaddada cewa ayyukan kakkaɓe dajin na ci gaba a Sambisa, da dutsen Mandara da Timbuktu Triangle domin murƙushe ragowar ƴan ta’adda Boko Haram da ISWAP a yankin Arewa maso Gabas.

A wani ɓangare guda, sojojin sun hallaka adadi mai yawa na ƴan bindiga a Jihar Zamfara a wani sumame na haɗin gwuiwar ƙasa da sama a sansanin shahararren shugaban ƴan bindiga Gwaska Ɗan Karmi a Ƙaramar Hukumar Maru. An ce rundunar sojin ƙasa, tare da tallafin Rundunar Sojin Sama, ta kai harin ne bayan bayanan sirri sun nuna cewa sama da ƴan bindiga 100 sun taru domin shirya hare-hare kan al’ummomi da hanyoyin isar da kayan soji.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Magidanci Ya Kashe Mutumin Da Yake Zargin Hulɗa Da Matarsa A Yobe

Magidanci Ya Kashe Mutumin Da Yake Zargin Hulɗa Da Matarsa A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.