Sojojin Nijeriya sun yi nasarar murƙushe wasu fitattun shugabannin ‘yan bindiga a Jihar Katsina, inda suka kashe da dama daga cikinsu tare da ƙwace makamai da kuma kuɗaɗen kudade a wani samame da suka kai a jihar.
Rahotanni sun nuna cewa wannan farmaki ya yi mummunar illa ga wata babbar ƙungiyar ‘yan bindiga da ke ƙarƙashin wani shugaba mai suna Muhammadu Fulani, wanda ake zargi da jagorantar hare-hare da satar mutane a yankin. 
A yayin aikin, sojojin sun samu nasarar kwato makamai daban-daban da kuɗi daga hannun ‘yan bindigar, lamarin da ake ganin zai rage ƙarfin su na ci gaba da aikata laifuka.
Mahukunta sun bayyana cewa wannan nasara wani babban ci gaba ne a ƙoƙarin da ake yi na kawar da matsalar ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.
Sun kuma jaddada kudurin ci gaba da gudanar da irin waɗannan hare-hare domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.















Discussion about this post