Rundunar Sojin Nijeriya ta Birgediya ta 12 sun kashe wani da ake zargin ɗan ta’adda ne tare da ƙwato makamai da harsasai yayin wani sumamen kwanton ɓauna da suka kai a dajin Adankolo da ke ƙaramar hukumar Lokoja a jihar Kogi.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da muƙaddashin mataimakin daraktan hulɗa da jama’a na Birgediya ta 12, Hassan Abdullahi, ya sanya wa hannu ranar Lahadi. Ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun sahihan bayanai kan motsin wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne a yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa dakarun rundunar kai agajin gaggawa sun yi kwanton ɓauna a wata hanyar da ake zargin masu laifin ke bi tun da sassafe ranar 10 ga Mayu, 2026. Bayan sun yi arangama da waɗanda ake zargin, an yi musayar wuta inda aka kashe ɗaya daga cikinsu yayin da sauran suka tsere cikin daji da raunukan harbin bindiga.
Bayan artabun, dakarun sun ƙwato bindigogi biyu ƙirar AK-47, da bindiga ƙirar gida guda ɗaya, sinƙin harsashi guda shida da harsasai 145 masu tsayin 7.62mm. Sauran kayayyakin da aka samu sun haɗa da bel ɗin harsasai na soji, da babur ƙirar Honda, da maganin Diclofenac, da wayoyin hannu guda uku, da power bank guda uku da kuma kuɗi naira 62,900.
Rundunar ta ce aikin na daga cikin matakan Operation TIGER PAW II da ake yi domin hana ‘yan ta’adda samun mafaka tare da ƙarfafa tsaro a Kogi da maƙwabtan jihohi. Ta kuma tabbatar da cewa dakaru na ci gaba da sintiri da bincike domin kamo waɗanda suka tsere bayan harin.















Discussion about this post