ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 324, Sun Ceto Mutane 610 Da Aka Sace A Watan Agusta

by Sadiq
1 week ago

Hedikwatar Tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta ce sojoji sun kashe ’yan ta’adda 324 tare da kama wasu mutane 373 da ake zargi da aikata laifuka a faɗin ƙasar a watan Agustan 2026.

Daraktan Sashen Yaɗa Labaran Ayyukan Sojoji, Manjo Janar Michael Onoja ne, ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin da yake yi wa manema labarai bayani kan ayyukan sojojin a watan Agusta.

Ya ce sojojin sun kuma ceto mutane 610 da aka yi garkuwa da su, yayin da ’yan ta’adda 201 suka miƙa wuya ga sojoji.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, an ƙwato bindigogi 88 da harsasai 2,077 yayin ayyukan sojojin.

Onoja ya kuma ce sojojin sun lalata wuraren tace man fetur ba bisa ƙa’ida ba guda 21 tare da ƙwato lita 686,800 na ɗanyen man fetur da aka sace.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Ya ce adadin ’yan ta’addan da ke miƙa wuya na nuna cewa matsin lambar da sojoji ke yi wa ƙungiyoyin masu aikata laifuka na ƙaruwa.

Adadin waɗanda suka miƙa wuya ya ƙaru daga 11 a watan Yuni zuwa 57 a Yuli, sannan ya kai 201 a watan Agusta.

Onoja ya ce sun ceto mutane 308, waɗanda mafi yawansu mata da yara ne daga dajin Kainji Lake National Park a ranar 5 ga watan Agusta.

Ya ce sojoji na ci gaba da gudanar da ayyuka a yankin da kewayen wurin domin hana ’yan ta’adda sake kai hare-hare da kuma samar da yanayin tsaro da zai bai wa mutanen da suka rasa matsugunansu damar komawa gidajensu.

Sojojin sun yi kira ga iyalan mutanen da aka yi garkuwa da su da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen ceto waɗanda har yanzu ke hannun masu garkuwa da mutane.

Onoja ya ce Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Olufemi Oluyede, ya jajirce wajen kare rayukan jama’a, ceto mutanen da aka yi garkuwa da su da kuma yaƙi da ta’addanci da sauran laifuka a faɗin ƙasar.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Halarci Taron Koli Na Kungiyar SCO

Shugaba Xi Ya Halarci Taron Koli Na Kungiyar SCO

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.