ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

by Leadership Hausa
4 years ago
'Yansanda

A ranar 11 ga watan Oktoba 2020 mun yi sharhi a kan takaddamar da ke tsakanin Rundunar ‘Yansanda da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda a kan shirin daukar sabbin ‘yansanda don fuskantar matsalolin tsaro a kasar nan.

A wannan karon Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda ta sanar da shirin fara daukar sabbin Kuratan sai Rundunar ‘Yansanda ta sana da cewa, al’umma su yi watsi da sanarwar.

  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu
  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Duk da Hukumar Kula da Aikin “Yansanda ta dakatar da shirin daukar Kuratan, amma hakan yana nuna cewa, har yanzu takaddamar da ke tsakanin Rundunar ‘Yansanda da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda yana bai kare ba.

ADVERTISEMENT

A kan haka mjka sake kawo muku sharkin da muka yi a waccan lokacin don gargadi a kan matsalar da takaddamar ka iya haifarwa ga bangaren tsaron kasar nan.

Yayin da ake fuskantar matsalar tsaro a sassan Nijeriya, wanda hakan ke haifar da kiraye-kirayen kara daukar matakin ganin an kawo karshen mastalolin gaba daya, amma sai gashi ‘yan Nijeriya sun wayi gari da takaddama a kan waye zai jagoranci daukar Kurata 1,000 aikin rundunar ‘yansandan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A kwanaki ne Kwamitin mutum uku na Kotun Daukaka Kara kakrkashin jarogarancin Maishari’a Olabisi Ige ta yanke hukuncin cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda da Rundunar ‘Yansanda basu da hurumin daukar Kruratan ‘yansanda a kasar nan.

Kotun ta zartas da cewa, Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda (PSC) ne kawai ke da hurumi na shari’a na daukar Kuratan ‘yansanda, a kan haka Kotun ta haramta daukar Kuratan da Rundunar ‘Yansanda ta jagoranta.

Hukumar Kula da Aikin ‘Yansandan ta maka Sufeton ‘Yansanda ne a kotu inda take kalubalantar daukar Kurata 10,000 da Rundunar ta jagoranta inda kotun ta zartas da cewa, Rundunar ‘yansanda bata da hurumin jagorantar daukar Kuratan, “Dauka, karin girma da korar ‘yansanda ba hakki ne na Rundunar ‘Yansanda ba, hakki ne na Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda.” In ji Kotun.

A kan haka Hukumar Kula da Aikin ‘Yansadan ta nemi kotu ta soke shirin da Rundunar ‘Yansanda ta yi na daukar Kuratan ‘yansanda a fadin kasar nan gaba daya.

Tun da farko a Mai Shari’a Inyang Ekwo na Babban Kotun Tarayya a hukuncin da ya yanke a ranar 2 ga watan Disamba 2019, ya kori karar da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansandan ta shigar ne, abin da ya sa suka daukaka karar, inda Kotun Daukaka Kara ta zartar da hukuncin da ya yi musu dadi.

Wannan jaridar na daukar takaddamar da ke tsakanin PSC da IGP a kan wanda yake da hurumin daukar Kuratan ‘yansanda a mastayin wani babbar tarnaki ga kokarin da ake yi na kawo karshen matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu.

A ra’ayinmu bai kamata a ce hukumomin gwamnati biyu sun shiga wannan takaddamar ba musamman ganin aikin da ke a gaban sun a tabbatar da tsaron al’umma a halin yanzu.

Mun damu matuka ganin yadda ake fustantar matsalar tsaro a sassan kasar nan amma bangaren rundunar tsaronta na takaddama a kan wanda yake da hurumin jagorantar daukar Kuratan ‘Yansanda a Nijeriya, wannan takaddamar na iya kawar da hankalinsu daga kokarin da ake yi na yaki da matsalar tsaro da ‘yan bindiga a Nijeriya.

Tabbas wannan takaddama abin takaici ne, ganin muna cikin lokacin da yakamata a hada karfi da karfe a yakin da ake yi da ‘yan bindiga.

Ra’ayi ya hadu a kan cewa, Nijeriya na bukatar karin ‘yansanda, don matakin Majalisar Dinkin Duniya shi ne na dan sanda daya aka ‘yan kasa 600.

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya na shekarar 2006 ya ayyana samar da ‘yansanda 300 ga ‘yan kasa 100,000.

An kuma lura da kasashe tara kawai suka iya samar da ‘yansanda 100 ga ‘yan kasa 100,000. Rahoton ya kara bayyana cewa, kasashen da suka fi kuka da wannan ka’ida suna yankin Asiya ta Yamma da Gabas da kuma Kudancin Turai.

A kwanan ne, Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya bayyana cewa, a jiharsa ‘yansanda 30 ke kula da kauyuka fiye da 100.

Har zuwa yau da muke maganar nan, Rundunar ‘Yansanda ba su fito sun karyata wannan bayani ba na Masari.
Ko ba komai maganar tana fitowa ne daga bakin Babban Jami’i mai kula da harkokin tsaron jihar, jihar da take fuskantar matsalolin tsaro wadda ta kai ga rasa rayuka da dukiyoyin al’umma da dama a ‘yan shekarun nan.

Ana tsananin fuskantar karancin jami’an ‘yansanda a Nijeriya, maimakon a fuskanci hanyoyin da za su kawo karshen wannan matsalar wanda hakan zai kara dawo da mutuncin rundunar sai gashi takaddamar wa zai jagoranci daukar Kurata ya turnuke kasa.

A ra’ayinmu wannan takaddamar tsakanin hukumomin biyu masu muhimmanci ga shirin tabbatar da tsaro a kasar nan yana nuna rashin sa ido ne daga gwamnati kuma yakamata a gaggauta daukar matakin warware matsalar.

Tabbas babu mai kokwanton cewa, matsalar tsaro na daga cikin manyan-manayn matsalolin da ke fuskantar kasar a wannan lokacin, saboda haka samun takaddama a tsakanin PSC da NPF abin takaici ne kwarai da gaske, musamman ganin harkokin ‘yanta’adda irinsu garkuwa da mutane, fyade da sauran ayyuykan masu aikata manyan laiffuka ya taukura a’lumma.

Muna Allah wadai da takaddamar neman girma tsakanin cibiyoyin gwamnatin guda biyu, kuma abin takaci ne ma’aikatar da ke kula da cibiyoyin biyu ta kasa samar da fahimtar juna a tsakanin su.

A kan haka muna kira da Ma’aikatar Kula Harkokin ‘Yansada ta shigo don samar da yanayin fahinta a tsakaninsu, ta haka za a samu tabbacin samar da isassun ‘yansanda don fuskantar matsalolin tsaro a fadin kasar nan.

'Yansanda
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.