ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddama Kan Shirin Daukar Sabbin ‘Yansanda

by Leadership Hausa
4 years ago
'Yansanda

A ranar 11 ga watan Oktoba 2020 mun yi sharhi a kan takaddamar da ke tsakanin Rundunar ‘Yansanda da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda a kan shirin daukar sabbin ‘yansanda don fuskantar matsalolin tsaro a kasar nan.

A wannan karon Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda ta sanar da shirin fara daukar sabbin Kuratan sai Rundunar ‘Yansanda ta sana da cewa, al’umma su yi watsi da sanarwar.

  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu
  • Chelsea Ta Nada Potter A Matsayin Sabon Kocinta

Duk da Hukumar Kula da Aikin “Yansanda ta dakatar da shirin daukar Kuratan, amma hakan yana nuna cewa, har yanzu takaddamar da ke tsakanin Rundunar ‘Yansanda da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda yana bai kare ba.

ADVERTISEMENT

A kan haka mjka sake kawo muku sharkin da muka yi a waccan lokacin don gargadi a kan matsalar da takaddamar ka iya haifarwa ga bangaren tsaron kasar nan.

Yayin da ake fuskantar matsalar tsaro a sassan Nijeriya, wanda hakan ke haifar da kiraye-kirayen kara daukar matakin ganin an kawo karshen mastalolin gaba daya, amma sai gashi ‘yan Nijeriya sun wayi gari da takaddama a kan waye zai jagoranci daukar Kurata 1,000 aikin rundunar ‘yansandan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A kwanaki ne Kwamitin mutum uku na Kotun Daukaka Kara kakrkashin jarogarancin Maishari’a Olabisi Ige ta yanke hukuncin cewa, Babban Sufeton ‘Yansanda da Rundunar ‘Yansanda basu da hurumin daukar Kruratan ‘yansanda a kasar nan.

Kotun ta zartas da cewa, Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda (PSC) ne kawai ke da hurumi na shari’a na daukar Kuratan ‘yansanda, a kan haka Kotun ta haramta daukar Kuratan da Rundunar ‘Yansanda ta jagoranta.

Hukumar Kula da Aikin ‘Yansandan ta maka Sufeton ‘Yansanda ne a kotu inda take kalubalantar daukar Kurata 10,000 da Rundunar ta jagoranta inda kotun ta zartas da cewa, Rundunar ‘yansanda bata da hurumin jagorantar daukar Kuratan, “Dauka, karin girma da korar ‘yansanda ba hakki ne na Rundunar ‘Yansanda ba, hakki ne na Hukumar Kula da Aikin ‘Yansanda.” In ji Kotun.

A kan haka Hukumar Kula da Aikin ‘Yansadan ta nemi kotu ta soke shirin da Rundunar ‘Yansanda ta yi na daukar Kuratan ‘yansanda a fadin kasar nan gaba daya.

Tun da farko a Mai Shari’a Inyang Ekwo na Babban Kotun Tarayya a hukuncin da ya yanke a ranar 2 ga watan Disamba 2019, ya kori karar da Hukumar Kula da Aikin ‘Yansandan ta shigar ne, abin da ya sa suka daukaka karar, inda Kotun Daukaka Kara ta zartar da hukuncin da ya yi musu dadi.

Wannan jaridar na daukar takaddamar da ke tsakanin PSC da IGP a kan wanda yake da hurumin daukar Kuratan ‘yansanda a mastayin wani babbar tarnaki ga kokarin da ake yi na kawo karshen matsalar tsaron da ake fuskanta a halin yanzu.

A ra’ayinmu bai kamata a ce hukumomin gwamnati biyu sun shiga wannan takaddamar ba musamman ganin aikin da ke a gaban sun a tabbatar da tsaron al’umma a halin yanzu.

Mun damu matuka ganin yadda ake fustantar matsalar tsaro a sassan kasar nan amma bangaren rundunar tsaronta na takaddama a kan wanda yake da hurumin jagorantar daukar Kuratan ‘Yansanda a Nijeriya, wannan takaddamar na iya kawar da hankalinsu daga kokarin da ake yi na yaki da matsalar tsaro da ‘yan bindiga a Nijeriya.

Tabbas wannan takaddama abin takaici ne, ganin muna cikin lokacin da yakamata a hada karfi da karfe a yakin da ake yi da ‘yan bindiga.

Ra’ayi ya hadu a kan cewa, Nijeriya na bukatar karin ‘yansanda, don matakin Majalisar Dinkin Duniya shi ne na dan sanda daya aka ‘yan kasa 600.

Rahoton Majalisar Dinkin Duniya na shekarar 2006 ya ayyana samar da ‘yansanda 300 ga ‘yan kasa 100,000.

An kuma lura da kasashe tara kawai suka iya samar da ‘yansanda 100 ga ‘yan kasa 100,000. Rahoton ya kara bayyana cewa, kasashen da suka fi kuka da wannan ka’ida suna yankin Asiya ta Yamma da Gabas da kuma Kudancin Turai.

A kwanan ne, Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya bayyana cewa, a jiharsa ‘yansanda 30 ke kula da kauyuka fiye da 100.

Har zuwa yau da muke maganar nan, Rundunar ‘Yansanda ba su fito sun karyata wannan bayani ba na Masari.
Ko ba komai maganar tana fitowa ne daga bakin Babban Jami’i mai kula da harkokin tsaron jihar, jihar da take fuskantar matsalolin tsaro wadda ta kai ga rasa rayuka da dukiyoyin al’umma da dama a ‘yan shekarun nan.

Ana tsananin fuskantar karancin jami’an ‘yansanda a Nijeriya, maimakon a fuskanci hanyoyin da za su kawo karshen wannan matsalar wanda hakan zai kara dawo da mutuncin rundunar sai gashi takaddamar wa zai jagoranci daukar Kurata ya turnuke kasa.

A ra’ayinmu wannan takaddamar tsakanin hukumomin biyu masu muhimmanci ga shirin tabbatar da tsaro a kasar nan yana nuna rashin sa ido ne daga gwamnati kuma yakamata a gaggauta daukar matakin warware matsalar.

Tabbas babu mai kokwanton cewa, matsalar tsaro na daga cikin manyan-manayn matsalolin da ke fuskantar kasar a wannan lokacin, saboda haka samun takaddama a tsakanin PSC da NPF abin takaici ne kwarai da gaske, musamman ganin harkokin ‘yanta’adda irinsu garkuwa da mutane, fyade da sauran ayyuykan masu aikata manyan laiffuka ya taukura a’lumma.

Muna Allah wadai da takaddamar neman girma tsakanin cibiyoyin gwamnatin guda biyu, kuma abin takaci ne ma’aikatar da ke kula da cibiyoyin biyu ta kasa samar da fahimtar juna a tsakanin su.

A kan haka muna kira da Ma’aikatar Kula Harkokin ‘Yansada ta shigo don samar da yanayin fahinta a tsakaninsu, ta haka za a samu tabbacin samar da isassun ‘yansanda don fuskantar matsalolin tsaro a fadin kasar nan.

'Yansanda
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.