A shekarar 1925, aka dawo da shi sarautar Hakimci tare da ba shi Hakimi mai kula da Sabon Garin Zariya. Cikin ikon Allah kuma sai ya taka muhimmiyar gudunmawa wajen gina Sabon Garin, Zariya, inda ya kafa makarantar Firamare, da kuma haifar da sababbin unguwanni kamar irisu Muchiya da kuma Dogon Bauchi daga shekarar 1927 zuwa 1930.
A shekarar 1937, sai tasirinsa ya bazu zuwa Kaduna, inda aka ba shi sarautar Magajin Garin Zazzau a lokacin Sarkin Zazzau Ja’afaru Ɗan Isiyaku shi ne yake mulkin ƙasar Zazzau. A shekarar 1943, ya fara shirin dasa itatuwa wanda ya kyautatawa shi ƙyawun gari ga samar da inuwa da kuma iska mai matuƙar amfani ga Ɗan Adam, daganan kuma sai ya ƙirƙiro lamarin ba da lambar gidaje ta haruffa da kuma lambobi, wanda hakan ko shakka babu shi tsarin nasa ya taimaka wajen tsara gari da kuma gyara harkokin gine-gine.
Sai kuma a shekarar 1956, ya yi matuƙar kafa tarihi inda ya zama mutum na farko daga sashen Arewa da ya zama Administrator wato (Shugaba) na Gwamnatin Ƙaramar Hukumar Kaduna. A waccan shekarar ce, sai Sarauniya Elizabeth ta II ta ba shi lambar yabo ta Member of the British Empire (O.B.E.) saboda gudunmawarsa da yake badawa wajen ci gaban al’ummarsa.
Ayyukan da Muhammadu Aminu Sambo ya gudanar tamkar ma sun wuce zamaninsa ne. Gudunmawar sa a ɓangaren limi, ga lamarin ci gaban Birane, da gudanarwa sun yi gaggrumin tasiri a Arewacin Nijeriya. Makarantun da ya kafa sun zama cibiyoyin ilimi a halin da ake ciki yanzu, kuma hangen nesan sa wajen tsara gari da kula da muhalli ya zama abin koyi ga shugabanni na gaba.
Ya rasu ne shekara ta 1961, ya bar tarihin gaskiya, jagoranci, da kuma sha’anin ci gaban rayuwar al’ummaci da abin zai yi tasirin da ba ayi tsammani ba. A yau, sunansa yana nuna cewa yana da ƙarfin ilimi, shugabanci mai hangen nesa, da ƙauna da kuma ƙoƙari a kowane lokaci sabpda da ci gaban al’ummar sa.
Mun kawo ƙarshen taihin wannan Bawan Allah Alhaji Muhammadu Sambo sai kuma idan Allah mai kow mai komai ya kai mu mako na gaba, za mu kawo maku wani sabon tarihin wani lamarin da ya faru, wanda mun san zai sa kuma ku ƙara ilimi wanda yake shi Kogi ne. Ni ma kai na ban san irin wand azan kawo maku ba sai wanda Allah ya bada damar ba ku. Mun kuma samo maku wannan tarihin ne daga Dandalin Tarihin Magabata.














Discussion about this post