ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Sarkin Zazzau Jafaru Dan Isyaku 1935-1959

by Idris Aliyu Daudawa
8 months ago
Zazzau

Bayan sun taru ne Sarkin ya fara jawabi kamar haka “wasu daga cikinku waɗanda suke kusa sun ji mummunan labarin abinda yake faruwa a garin Zangon Kataf. Dan haka ina umurtar kowa daga cikin ku ya shirya ya kuma tabbatar da cewar gobe da safe kafin ƙarfe 9:00 na safe yana cikin mota. Duk wanda ya gaza bin wannan umurnin ya jira daga baya ya amshi kuɗin mota wurin Wali Umaru Hakimin Lere ya same mu a Zangon Kataf.

Kamar yadda Magajin Busa ya ce kowa ya bi wannan umurni na Mallam Jafaru, har da ma Jakadu duk sun kasance a mota kafin ƙarfe 9:00 na safe. Kimanin ƙarfe 9:00 daidai Sarkin Zazzau Mallam Jafaru ya fito daga masaukin shi da rawani mai haske akan shi, ya kuma rufe kan shi da ƙoƙuwar alkyabba. A hannunshi na hagu Kuma yana riƙe da Dala’ilu, hannun shi na dama kuma yana riƙe da farin charbi. Da fitowar shi bai ma kowa magana ba alama kawai ya yi da hannu na idan motarsa tayi gaba duk sauran ayarin motocin su bishi a baya.

  • Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Illolin Da Yawace-yawacen Mata Ke Haifarwa Ga Zamantakewar Aure

Mallam Jafaru ya bar Lere ya nufi Zangon Kataf kai tsaye. A wancan lokacin, lokacin rani ne hanyar data haɗa Lere da Zangon Kataf tana cikin mummunan yanayi. Saboda munin wancan hanyar tafiyar daga Lere zuwa Zangon Kataf yana ɗaukar Sarkin da tawagar shi tsawon tafiyar yini ɗaya sannan ya kai kusa da garin Zangon. Motar Sarkin da tawagar shi sun tsaya a Gonar Ganye, wacce take kusa da garin Zangon Kataf. Cikin hanzari Baraya Hamisu ya fito ya buɗe ma Sarkin ƙofa, Mallam Jafaru ya fito daga mota, suma yan tawagar Sarkin suka fito daga motocinsu amna banda tsoffafi da Jakadu.

ADVERTISEMENT

Sarkin Zazzau Mallam Jafaru Dan Isyaku, ya fuskanci garin Zangon Kataf yayi ta addu’a kusan tsawon mintina arba’in sauran yan tawagar Sarki na amsawa da Amin. Bayan Sarkin na Zazzau ya kammala addu’oin na shi ya juyo wurin mutane ya amsa gaisuwa, sannan ya tabbatar musu da cewar da yaddar Allah babu abinda zai faru. Suka kintsa suka shiga garin Zangon Kataf. Mallam Jafaru Dan Isyaku ya umurci kowa ya koma bayan shi, shi ne zai shiga gaba ya shugabanci wannan tawagar a shiga Zango.

Shigowa garin Zango da Mallam Jafaru ya yi, ya yi mutuƙar girgiza kabilun garin. Sarkin Zazzau Mallam Jafaru da ya shigo garin yaga sun kewaye ko ina a garin. Izzarshi da kwarjinin shi ya yi mutuƙar yin tasiri a wurinsu. Waɗannan kabilu masu ƙoƙarin tada ƙayar baya, suna ganin Sarkin da tawagar shi suka tarwatse sukai cikin daji a guje. Nan take Sarkin ya umurci makaɗan Sarki da yan bindiga su fara aikinsu. Ƴan bindiga suka fara harbi a sama, makaɗa da mabusa suka shiga aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Nan take Hausawan  garin Zango suka shiga fitowa daga gidajensu, wasu daga mavoyarsu. Al’umma suka shiga murna da farin ciki suna ma Sarkin jinjina. Mai son ya samu cikkakken labarin nan sai ya duba littafi mai suna Mallam Jafaru Dan Isyaku The Great Emir Of Zazzau shafi 436-439 wanda Usman Dalhatu  iliyasu ya rubuta.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.