ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Sarkin Zazzau Jafaru Dan Isyaku 1935-1959

by Idris Aliyu Daudawa
5 months ago
Zazzau

Bayan sun taru ne Sarkin ya fara jawabi kamar haka “wasu daga cikinku waɗanda suke kusa sun ji mummunan labarin abinda yake faruwa a garin Zangon Kataf. Dan haka ina umurtar kowa daga cikin ku ya shirya ya kuma tabbatar da cewar gobe da safe kafin ƙarfe 9:00 na safe yana cikin mota. Duk wanda ya gaza bin wannan umurnin ya jira daga baya ya amshi kuɗin mota wurin Wali Umaru Hakimin Lere ya same mu a Zangon Kataf.

Kamar yadda Magajin Busa ya ce kowa ya bi wannan umurni na Mallam Jafaru, har da ma Jakadu duk sun kasance a mota kafin ƙarfe 9:00 na safe. Kimanin ƙarfe 9:00 daidai Sarkin Zazzau Mallam Jafaru ya fito daga masaukin shi da rawani mai haske akan shi, ya kuma rufe kan shi da ƙoƙuwar alkyabba. A hannunshi na hagu Kuma yana riƙe da Dala’ilu, hannun shi na dama kuma yana riƙe da farin charbi. Da fitowar shi bai ma kowa magana ba alama kawai ya yi da hannu na idan motarsa tayi gaba duk sauran ayarin motocin su bishi a baya.

  • Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Illolin Da Yawace-yawacen Mata Ke Haifarwa Ga Zamantakewar Aure

Mallam Jafaru ya bar Lere ya nufi Zangon Kataf kai tsaye. A wancan lokacin, lokacin rani ne hanyar data haɗa Lere da Zangon Kataf tana cikin mummunan yanayi. Saboda munin wancan hanyar tafiyar daga Lere zuwa Zangon Kataf yana ɗaukar Sarkin da tawagar shi tsawon tafiyar yini ɗaya sannan ya kai kusa da garin Zangon. Motar Sarkin da tawagar shi sun tsaya a Gonar Ganye, wacce take kusa da garin Zangon Kataf. Cikin hanzari Baraya Hamisu ya fito ya buɗe ma Sarkin ƙofa, Mallam Jafaru ya fito daga mota, suma yan tawagar Sarkin suka fito daga motocinsu amna banda tsoffafi da Jakadu.

ADVERTISEMENT

Sarkin Zazzau Mallam Jafaru Dan Isyaku, ya fuskanci garin Zangon Kataf yayi ta addu’a kusan tsawon mintina arba’in sauran yan tawagar Sarki na amsawa da Amin. Bayan Sarkin na Zazzau ya kammala addu’oin na shi ya juyo wurin mutane ya amsa gaisuwa, sannan ya tabbatar musu da cewar da yaddar Allah babu abinda zai faru. Suka kintsa suka shiga garin Zangon Kataf. Mallam Jafaru Dan Isyaku ya umurci kowa ya koma bayan shi, shi ne zai shiga gaba ya shugabanci wannan tawagar a shiga Zango.

Shigowa garin Zango da Mallam Jafaru ya yi, ya yi mutuƙar girgiza kabilun garin. Sarkin Zazzau Mallam Jafaru da ya shigo garin yaga sun kewaye ko ina a garin. Izzarshi da kwarjinin shi ya yi mutuƙar yin tasiri a wurinsu. Waɗannan kabilu masu ƙoƙarin tada ƙayar baya, suna ganin Sarkin da tawagar shi suka tarwatse sukai cikin daji a guje. Nan take Sarkin ya umurci makaɗan Sarki da yan bindiga su fara aikinsu. Ƴan bindiga suka fara harbi a sama, makaɗa da mabusa suka shiga aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Nan take Hausawan  garin Zango suka shiga fitowa daga gidajensu, wasu daga mavoyarsu. Al’umma suka shiga murna da farin ciki suna ma Sarkin jinjina. Mai son ya samu cikkakken labarin nan sai ya duba littafi mai suna Mallam Jafaru Dan Isyaku The Great Emir Of Zazzau shafi 436-439 wanda Usman Dalhatu  iliyasu ya rubuta.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.