ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Sarkin Zazzau Jafaru Dan Isyaku 1935-1959

by Idris Aliyu Daudawa
4 months ago
Zazzau

Bayan sun taru ne Sarkin ya fara jawabi kamar haka “wasu daga cikinku waɗanda suke kusa sun ji mummunan labarin abinda yake faruwa a garin Zangon Kataf. Dan haka ina umurtar kowa daga cikin ku ya shirya ya kuma tabbatar da cewar gobe da safe kafin ƙarfe 9:00 na safe yana cikin mota. Duk wanda ya gaza bin wannan umurnin ya jira daga baya ya amshi kuɗin mota wurin Wali Umaru Hakimin Lere ya same mu a Zangon Kataf.

Kamar yadda Magajin Busa ya ce kowa ya bi wannan umurni na Mallam Jafaru, har da ma Jakadu duk sun kasance a mota kafin ƙarfe 9:00 na safe. Kimanin ƙarfe 9:00 daidai Sarkin Zazzau Mallam Jafaru ya fito daga masaukin shi da rawani mai haske akan shi, ya kuma rufe kan shi da ƙoƙuwar alkyabba. A hannunshi na hagu Kuma yana riƙe da Dala’ilu, hannun shi na dama kuma yana riƙe da farin charbi. Da fitowar shi bai ma kowa magana ba alama kawai ya yi da hannu na idan motarsa tayi gaba duk sauran ayarin motocin su bishi a baya.

  • Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Illolin Da Yawace-yawacen Mata Ke Haifarwa Ga Zamantakewar Aure

Mallam Jafaru ya bar Lere ya nufi Zangon Kataf kai tsaye. A wancan lokacin, lokacin rani ne hanyar data haɗa Lere da Zangon Kataf tana cikin mummunan yanayi. Saboda munin wancan hanyar tafiyar daga Lere zuwa Zangon Kataf yana ɗaukar Sarkin da tawagar shi tsawon tafiyar yini ɗaya sannan ya kai kusa da garin Zangon. Motar Sarkin da tawagar shi sun tsaya a Gonar Ganye, wacce take kusa da garin Zangon Kataf. Cikin hanzari Baraya Hamisu ya fito ya buɗe ma Sarkin ƙofa, Mallam Jafaru ya fito daga mota, suma yan tawagar Sarkin suka fito daga motocinsu amna banda tsoffafi da Jakadu.

ADVERTISEMENT

Sarkin Zazzau Mallam Jafaru Dan Isyaku, ya fuskanci garin Zangon Kataf yayi ta addu’a kusan tsawon mintina arba’in sauran yan tawagar Sarki na amsawa da Amin. Bayan Sarkin na Zazzau ya kammala addu’oin na shi ya juyo wurin mutane ya amsa gaisuwa, sannan ya tabbatar musu da cewar da yaddar Allah babu abinda zai faru. Suka kintsa suka shiga garin Zangon Kataf. Mallam Jafaru Dan Isyaku ya umurci kowa ya koma bayan shi, shi ne zai shiga gaba ya shugabanci wannan tawagar a shiga Zango.

Shigowa garin Zango da Mallam Jafaru ya yi, ya yi mutuƙar girgiza kabilun garin. Sarkin Zazzau Mallam Jafaru da ya shigo garin yaga sun kewaye ko ina a garin. Izzarshi da kwarjinin shi ya yi mutuƙar yin tasiri a wurinsu. Waɗannan kabilu masu ƙoƙarin tada ƙayar baya, suna ganin Sarkin da tawagar shi suka tarwatse sukai cikin daji a guje. Nan take Sarkin ya umurci makaɗan Sarki da yan bindiga su fara aikinsu. Ƴan bindiga suka fara harbi a sama, makaɗa da mabusa suka shiga aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Nan take Hausawan  garin Zango suka shiga fitowa daga gidajensu, wasu daga mavoyarsu. Al’umma suka shiga murna da farin ciki suna ma Sarkin jinjina. Mai son ya samu cikkakken labarin nan sai ya duba littafi mai suna Mallam Jafaru Dan Isyaku The Great Emir Of Zazzau shafi 436-439 wanda Usman Dalhatu  iliyasu ya rubuta.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.