ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Sarkin Zazzau Jafaru Dan Isyaku 1935-1959

by Idris Aliyu Daudawa
5 months ago
Zazzau

Bayan sun taru ne Sarkin ya fara jawabi kamar haka “wasu daga cikinku waɗanda suke kusa sun ji mummunan labarin abinda yake faruwa a garin Zangon Kataf. Dan haka ina umurtar kowa daga cikin ku ya shirya ya kuma tabbatar da cewar gobe da safe kafin ƙarfe 9:00 na safe yana cikin mota. Duk wanda ya gaza bin wannan umurnin ya jira daga baya ya amshi kuɗin mota wurin Wali Umaru Hakimin Lere ya same mu a Zangon Kataf.

Kamar yadda Magajin Busa ya ce kowa ya bi wannan umurni na Mallam Jafaru, har da ma Jakadu duk sun kasance a mota kafin ƙarfe 9:00 na safe. Kimanin ƙarfe 9:00 daidai Sarkin Zazzau Mallam Jafaru ya fito daga masaukin shi da rawani mai haske akan shi, ya kuma rufe kan shi da ƙoƙuwar alkyabba. A hannunshi na hagu Kuma yana riƙe da Dala’ilu, hannun shi na dama kuma yana riƙe da farin charbi. Da fitowar shi bai ma kowa magana ba alama kawai ya yi da hannu na idan motarsa tayi gaba duk sauran ayarin motocin su bishi a baya.

  • Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
  • Illolin Da Yawace-yawacen Mata Ke Haifarwa Ga Zamantakewar Aure

Mallam Jafaru ya bar Lere ya nufi Zangon Kataf kai tsaye. A wancan lokacin, lokacin rani ne hanyar data haɗa Lere da Zangon Kataf tana cikin mummunan yanayi. Saboda munin wancan hanyar tafiyar daga Lere zuwa Zangon Kataf yana ɗaukar Sarkin da tawagar shi tsawon tafiyar yini ɗaya sannan ya kai kusa da garin Zangon. Motar Sarkin da tawagar shi sun tsaya a Gonar Ganye, wacce take kusa da garin Zangon Kataf. Cikin hanzari Baraya Hamisu ya fito ya buɗe ma Sarkin ƙofa, Mallam Jafaru ya fito daga mota, suma yan tawagar Sarkin suka fito daga motocinsu amna banda tsoffafi da Jakadu.

ADVERTISEMENT

Sarkin Zazzau Mallam Jafaru Dan Isyaku, ya fuskanci garin Zangon Kataf yayi ta addu’a kusan tsawon mintina arba’in sauran yan tawagar Sarki na amsawa da Amin. Bayan Sarkin na Zazzau ya kammala addu’oin na shi ya juyo wurin mutane ya amsa gaisuwa, sannan ya tabbatar musu da cewar da yaddar Allah babu abinda zai faru. Suka kintsa suka shiga garin Zangon Kataf. Mallam Jafaru Dan Isyaku ya umurci kowa ya koma bayan shi, shi ne zai shiga gaba ya shugabanci wannan tawagar a shiga Zango.

Shigowa garin Zango da Mallam Jafaru ya yi, ya yi mutuƙar girgiza kabilun garin. Sarkin Zazzau Mallam Jafaru da ya shigo garin yaga sun kewaye ko ina a garin. Izzarshi da kwarjinin shi ya yi mutuƙar yin tasiri a wurinsu. Waɗannan kabilu masu ƙoƙarin tada ƙayar baya, suna ganin Sarkin da tawagar shi suka tarwatse sukai cikin daji a guje. Nan take Sarkin ya umurci makaɗan Sarki da yan bindiga su fara aikinsu. Ƴan bindiga suka fara harbi a sama, makaɗa da mabusa suka shiga aikinsu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Nan take Hausawan  garin Zango suka shiga fitowa daga gidajensu, wasu daga mavoyarsu. Al’umma suka shiga murna da farin ciki suna ma Sarkin jinjina. Mai son ya samu cikkakken labarin nan sai ya duba littafi mai suna Mallam Jafaru Dan Isyaku The Great Emir Of Zazzau shafi 436-439 wanda Usman Dalhatu  iliyasu ya rubuta.

Zazzau
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

Muhimmancin Abinci Ga Lafiya Ɗan’Adam

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.