ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illolin Da Yawace-yawacen Mata Ke Haifarwa Ga Zamantakewar Aure

by Rabi'at Sidi Bala
6 months ago
Mata

Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban, wadanda suka shafi al’umma. Ciki sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu.

Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da abin da ya shafi yawan yawace-yawace da wasu matan ke yi, duba da yadda wasu matan ke da dabi’ar yawace-yawace a kullum zuwa gidajen makofta, musamman wadanda suke da aure, domin su yi hira.

  • Babu Wani Annabi Mai Daraja Kusa Da Ta Muhammad Rasulullah (SAW)
  • Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

Dalilin hakan ya sa wannan shafi jin ta bakin wasu daga cikin ma’abota shafin game da wannan batu; “Ko me za a ce akan hakan?, me yake janyo haka, kuma me ya sa?, ko akwai wasu illoli ko amfanin yawan yawace-yawace?.

ADVERTISEMENT

Ga dai bayanan nasu kamar haka;

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor), daga Jihar Kano:

LABARAI MASU NASABA

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

Kwarai akwai, musamman sababbin unguwanni, nan sai ki samu sama da mace goma sun taru gidan mace daya. San gantali ne da zaman gulma kawai. Ba shi da amfani karshe ma dai a koyo wasu dabi’u na daban. Su daina tun kan su girgide aurensu.

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Tabbas hakan ana samun wasu matan da irin wannan dabi’a, kuma hakan na haifar da matsaloli da dama a zamantakewa. To, magana ta gaskiya sakacin mai gida a lokuta da dama shi ke jawo wannan matsala, to amma a wasu lokutan matan suna yin hakan bada sanin maigidan ba wato suna yin satar fita. Hakika illolin suna da yawa, na farko za ta zama munafuka wasu lokutan kuma a dora mata sata da dai sauran su. amfani kuwa babu wani amfani a wannan dabi’a face zubar da mutunci. To, shawara ta a nan ita ce su ji tsoron Allah matan su daina wannan dabi’a, maza kuma ya kamata mutum yake kula da abubuwan dake faruwa a gidan sa sosai.

 

Sunana Princess Fatima Mazadu, Gomben Nijeriya:

Yin hakan ba abu ne me kyau ba, ya kamata mace ta kare hakkin aurenta ba yawace-yawace ba. Hira ba dole bane sai an fita yi, tun da akwai karance-karance na alkur’ani ko littatafai ko sauraron rediyo, ba amfanin tsallake muhalli zuwa na wani daban. Ko da mutun bai ce kina takura shi ba, ko dan gulma da hirar karya, da koyan sababbin dabi’au marasa kyau, da munafunci, ke kanki bai dace ba a tsarance. Ya kan janyo rashin kamun Kai, zubda mutunci da da-na-sani, saboda a cikin magana zat a fadi sirrinta a zo ana yayatawa tana takaici. Wata ma aurenta har mutuwa yake yi, saboda ba kowa zai dauki mace mai yawan yawo da mutunci ba. Shawarata a nan mata a rika hakuri a gidan aure, in damuwace ki roki Allah, kowa da irin tasa jarabawar, ki rungumi taki hannu bibbiyu, saboda ki tsira da mutuncinki. Allah ya yasa mu dace.

 

Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:

Hakan bai kamata ba, saboda duk hirar da mace za ta yi a cikin gida tare da mutane karshe a kawo hirar wata, ko a hada wani munafurcin, musamman idan mace tana da kishiya ko facala. Ba za ta zauna a gidanta ba, sai dai ta rika yawo tana fadar halayyar ta ko tana bata ta. Hakan yana kawo matsaloli da yawa, wani zai iya raba aurenta dalilin yawo aure yakan iya mutuwa. Shawarata macen aure ta zauna a gidanta ta fahimci aurenta, ta fuskanci aurenta, da yi wa mijinta biyayya, in sana’a take ta mayar da hankakinta a kai ya fi yawo da yawan shiga makota da gidajen mutane.

 

Sunana Muktari Sabo, Jahun Jihar Jigawa:

Tabbas akwai mata masu irin wannan dabi’a ta yawace-yawace wanda hakan ba daidai bane, ko da shiga gidan makwafta ne. Rashin girmama aure da kuma rashin sanin darajar kai shi ke janyo hakan, Illar wannan shi ne zai sa mace ta zamo mai hada husuma da kuma rashin godiya a gidanta. Sannan ga zubewar darajarta da ta ‘ya’yanta a idon mutane. Shawara a nan shi ne mata masu wannan hali su ji tsoron Allah, su sani hakan yana jawo fushin Allah subhanahu wa ta’ala.

 

Sunana Anas Bn Malik, Achilafiya, Karamar Hukumar Ƴankwashi, Jihar Jigawa:

Yawace-yawacen mata zuwa gidajen makwabta na iya zama al’ada mai kyau idan ana yin sa cikin mutunci da iyaka, domin yana karfafa zumunci, taimako da musayar ilimi. Amma idan ya wuce kima, yana iya jawo matsaloli kamar bata lokaci, sakaci da gida, shiga cikin gulma ko rikici, da kuma karya sirri. Sau da yawa dalilan da ke janyo hakan sun hada da; rashin aikin yi, neman nishadi, ko bukatar goyon bayan al’umma. Don haka shawarar da ta fi dacewa ita ce a daidaita wannan dabi’a: a tsara lokaci, a mutunta iyaka da sirrin makwafta, a guji gulma, sannan a mayar da hankali kan nauyin gida da tarbiyya. Wannan zai sa zumunci ya dore ba tare da matsala ba.

 

Sunana Aisha T. Bello, daga Jihar Kaduna:

Wasu gaskiya ya fara tun daga gida kafin su yi aure, kodayaushe in ka je basa gida sai gidan makota basa iya zama a gida ko kadan. Gaskiya sabo ne tun kafi aure iyaye basa magana shi ne har gidan miji, mace bata iya zama dakinta. Gaskiya hakan ba shi da wani amfani ko kadan. Shawarata ga masu irin wanan hali dan Allah su daina, ba shi da wani anfani yin hakan. Kuma iyaye su yi kokarin hana wanan yawon tun kafin su ba da auren ‘yar su, saboda yara amana ce Allah ya basu, Allah ya bamu ikon gyarawa (Amin).

 

Sunana Muhammad Isah Zareku, Miga A Jihar Jigawa:

A gaskiya wannan tana faruwa za ka ga mata sun ki zaman gidan aurensu suna shiga gidajen makwafta ba dan komai ba sai don hira da kuma zancen mutane kawai. Hakan yana kawo matsala ka ga mace taki zaman gidanta kawai don son zancen mutane. Kuma hakan yana kai su gidan makwafta ne don munafurci. Illolinsa ya fi yawa saboda a wannan shige da fice na shiga makwafta yake kawo rashin jituwa a makwabta, kuma ni a nawa tunanin ba shi da wani amfani yawan shiga gidan makwafta. Shawara a nan ita ce, mace ta zauna a gidanta duk wacce za ta je wajenta ita zaman auren take, don me ya sa za ki bar naki gidan ki tafi nata haka kawai.

Mata
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A 29-05-2027
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

MASU ALAKA

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
Taskira

Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Taskira

Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

May 24, 2026
Mata
Taskira

Aure Ba Sana’a:Imani Ko Ganganci?

May 16, 2026
Next Post
Borno Da Kano Sun Zama Zakaru A Gasar Karatun Alƙur’ani Ta Ƙasa Ta 2025

Borno Da Kano Sun Zama Zakaru A Gasar Karatun Alƙur’ani Ta Ƙasa Ta 2025

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.