ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihinta Na Jure Wahalhalu Ya Sa Kasar Sin Samun Karfin Zuci

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Jiya, manyan kusoshin kasar Sin sun kira wani taro don tattauna batun raya tattalin arziki, inda suka sa ran cika burikan da aka tsara, ta fuskar raya tattalin arziki da zaman al’umma a shekarar 2024. Kana sun gabatar da shirin raya tattalin arzikin kasar a shekarar 2025, mai kunshe da matakan harkar kudi masu yakini, da na raya kirkire-kirkire a fannin kimiyya da fasaha da masana’antu, da sa kaimi ga aikin sayayya, da dai makamantansu.

 

Wadannan matakai masu yakini sun sa mutane masu sayen hannayen jari na kasashe daban daban, yin imani da yanayin tattalin arzikin Sin. A jiya, ma’aunin darajar hannayen jarin kamfanonin kasar Sin a kasar Amurka da aka san shi da NASDAQ Golden Dragon China, da kuma ma’aunin Hang Seng na yankin Hong Kong na kasar Sin sun karu sosai. Kana a yau, darajar hannayen jarin kamfanoni fiye da 5200 dake kasuwar babban yankin kasar Sin su ma sun yi ta karuwa.

ADVERTISEMENT
  • Jami’ar Kwara Ta Rage Wa Masu Bukata Ta Musamman Kudin Karatu
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Kayar Da APC A 2027 Kamar Yadda Aka Yi Wa NPP A Ghana – PDP

Yadda manufofin kasar Sin a fannin tattalin arziki suka haifar da tasiri mai yakini a kasuwannin duniya bai ba mutane mamaki ba, saboda tun kafin kaddamar da sabbin matakan bunkasa tattalin arziki a kasar Sin, kwararru masu nazarin tattalin arzikin Sin sun dade suna nuna wa kasar Sin cikakken imani kan makomar tattalin arzikinta. A ganinsu, kasar Sin ta iya daidaita manyan tsare-tsaren tattalin arziki yadda take bukata, abin da ya sa ta kasancewa cikin yanayi mai karko duk lokacin da aka samu tangal-tangal na yanayin tattalin arzikin duniya. Wannan ra’ayi ya zama daya da abun da wani sharhin da aka wallafa a jaridar “The Guardians” ta kasar Najeriya a kwanakin baya ya kunsa, inda aka ce, yadda gwamnatin kasar Sin ke tinkarar kalubaloli cikin yakini, ya sa ta samun cikakkiyar jajircewa a fannin raya tattalin arziki, da samar da gudunmowa ga farfadowar tattalin arzikin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Hakika, kafin a yi imani da wani mutum ko wata kasa, dole ne ya/ta zama mai cike da imani da kai. A wajen wani taron neman tattara shawarwari daga manyan jami’an jam’iyyu daban daban na kasar Sin, da ya gudana a kasar a kwanan nan, shugaba Xi Jinping na Sin ya jaddada muhimmancin nuna imani kan samun ci gaban tattalin arziki. To sai dai kuma ko ta yaya za a iya samun imanin? Shugaba Xi ya ambaci fannoni 2: wato na farko, idan an yi bitar ainihin yanayin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, za a ga yana da tushe mai inganci, kana yanayi mai armashi da yake ciki bai taba canzawa ba. Na biyu, idan an duba tarihin kasar Sin, za a ga ba a taba rasa kalubalolin da ta fuskanta ba, sai dai hakan bai hana kasar samun ci gaba a kai a kai ba.

 

Maganar shugaba Xi ta tunatar mana da wani bidiyo, wanda mataimakiyar ministan harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta watsa kan shafin yanar gizo na sada zumunta, bayan da kasar Amurka ta kaddamar da takunkumi kan kayan latironi na Chip kirar kasar Sin a kwanan nan. Cikin bidiyon, an nuna yadda sabuwar kasar Sin ta samu nasarar kirkiro sabbin fasahohi masu muhimmanci, duk da takunkumai na tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, da kasashen yamma suka saka mata, tun bayan kafuwar kasar a shekarar 1949. Inda taken bidiyon shi ne: Wanda bai samu nasarar kashe ka ba, zai sa ka samun karin ci gaba. Wannan jimla ta takaita tarihin kasar Sin na raya kanta, tare da jure dimbin wahalhalu, wanda ya zama dalilin karfin zucin kasar a fannin tinkarar kalubaloli masu alaka da siyasa da tattalin arziki na duniya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
Tinubu Ya Nada Sabon Akanta Janar Na Kasa

Tinubu Ya Nada Sabon Akanta Janar Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.