ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihinta Na Jure Wahalhalu Ya Sa Kasar Sin Samun Karfin Zuci

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Jiya, manyan kusoshin kasar Sin sun kira wani taro don tattauna batun raya tattalin arziki, inda suka sa ran cika burikan da aka tsara, ta fuskar raya tattalin arziki da zaman al’umma a shekarar 2024. Kana sun gabatar da shirin raya tattalin arzikin kasar a shekarar 2025, mai kunshe da matakan harkar kudi masu yakini, da na raya kirkire-kirkire a fannin kimiyya da fasaha da masana’antu, da sa kaimi ga aikin sayayya, da dai makamantansu.

 

Wadannan matakai masu yakini sun sa mutane masu sayen hannayen jari na kasashe daban daban, yin imani da yanayin tattalin arzikin Sin. A jiya, ma’aunin darajar hannayen jarin kamfanonin kasar Sin a kasar Amurka da aka san shi da NASDAQ Golden Dragon China, da kuma ma’aunin Hang Seng na yankin Hong Kong na kasar Sin sun karu sosai. Kana a yau, darajar hannayen jarin kamfanoni fiye da 5200 dake kasuwar babban yankin kasar Sin su ma sun yi ta karuwa.

ADVERTISEMENT
  • Jami’ar Kwara Ta Rage Wa Masu Bukata Ta Musamman Kudin Karatu
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Kayar Da APC A 2027 Kamar Yadda Aka Yi Wa NPP A Ghana – PDP

Yadda manufofin kasar Sin a fannin tattalin arziki suka haifar da tasiri mai yakini a kasuwannin duniya bai ba mutane mamaki ba, saboda tun kafin kaddamar da sabbin matakan bunkasa tattalin arziki a kasar Sin, kwararru masu nazarin tattalin arzikin Sin sun dade suna nuna wa kasar Sin cikakken imani kan makomar tattalin arzikinta. A ganinsu, kasar Sin ta iya daidaita manyan tsare-tsaren tattalin arziki yadda take bukata, abin da ya sa ta kasancewa cikin yanayi mai karko duk lokacin da aka samu tangal-tangal na yanayin tattalin arzikin duniya. Wannan ra’ayi ya zama daya da abun da wani sharhin da aka wallafa a jaridar “The Guardians” ta kasar Najeriya a kwanakin baya ya kunsa, inda aka ce, yadda gwamnatin kasar Sin ke tinkarar kalubaloli cikin yakini, ya sa ta samun cikakkiyar jajircewa a fannin raya tattalin arziki, da samar da gudunmowa ga farfadowar tattalin arzikin duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Hakika, kafin a yi imani da wani mutum ko wata kasa, dole ne ya/ta zama mai cike da imani da kai. A wajen wani taron neman tattara shawarwari daga manyan jami’an jam’iyyu daban daban na kasar Sin, da ya gudana a kasar a kwanan nan, shugaba Xi Jinping na Sin ya jaddada muhimmancin nuna imani kan samun ci gaban tattalin arziki. To sai dai kuma ko ta yaya za a iya samun imanin? Shugaba Xi ya ambaci fannoni 2: wato na farko, idan an yi bitar ainihin yanayin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, za a ga yana da tushe mai inganci, kana yanayi mai armashi da yake ciki bai taba canzawa ba. Na biyu, idan an duba tarihin kasar Sin, za a ga ba a taba rasa kalubalolin da ta fuskanta ba, sai dai hakan bai hana kasar samun ci gaba a kai a kai ba.

 

Maganar shugaba Xi ta tunatar mana da wani bidiyo, wanda mataimakiyar ministan harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta watsa kan shafin yanar gizo na sada zumunta, bayan da kasar Amurka ta kaddamar da takunkumi kan kayan latironi na Chip kirar kasar Sin a kwanan nan. Cikin bidiyon, an nuna yadda sabuwar kasar Sin ta samu nasarar kirkiro sabbin fasahohi masu muhimmanci, duk da takunkumai na tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, da kasashen yamma suka saka mata, tun bayan kafuwar kasar a shekarar 1949. Inda taken bidiyon shi ne: Wanda bai samu nasarar kashe ka ba, zai sa ka samun karin ci gaba. Wannan jimla ta takaita tarihin kasar Sin na raya kanta, tare da jure dimbin wahalhalu, wanda ya zama dalilin karfin zucin kasar a fannin tinkarar kalubaloli masu alaka da siyasa da tattalin arziki na duniya. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027
  • Sulaiman
    Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?
  • Sulaiman
    Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan
  • Sulaiman
    Mariya Mahmoud: Aiki A karkashin Jagorancin Wike

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Next Post
Tinubu Ya Nada Sabon Akanta Janar Na Kasa

Tinubu Ya Nada Sabon Akanta Janar Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mariya Mahmoud: Aiki A karkashin Jagorancin Wike

June 15, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Gwamnatin Kano Ta Ware Naira Biliyan 1.5 Domin Aurar Da Ma’aurata 1,500

June 15, 2026
Sin Na Gina Karfin Sojinta Ne Saboda Kare Moriyar Tsaron Kasa

Sin Na Gina Karfin Sojinta Ne Saboda Kare Moriyar Tsaron Kasa

June 15, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Shari’ar Fiye Da Mutane 400 Da Ake Zargi Da Ta’addanci A Abuja

June 15, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

June 15, 2026
Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

Aminu Bayero Ya Samu Nakasu Ta Ɓangaren Siyasa

June 15, 2026
Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

Beijing: An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Game Da Gina JKS

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.