ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Masu Ruwa da Tsaki na Arewa maso Yamma Zai Zama Hanyar Bunkasa Yankin — Shettima 

by Shehu Yahaya and Sulaiman
4 months ago
Shettima

Jigo a jam’iyyar APC a shiyyar Arewa maso Yamma, Ambasada Usman Yerima Shettima, ya bayyana taron masu ruwa da tsaki na Arewa maso Yamma da aka gudanar a Kaduna a matsayin wata muhimmiyar hanya da za ta taimaka wajen ciyar da yankin gaba da kuma magance dimbin ƙalubalen da ke addabar yankin.

 

Honarabul Yerima ya ce, duba da irin matsalolin tsaro, tattalin arziki da zamantakewa da yankin Arewa maso Yamma ke fuskanta, babu shakka irin wannan taro zai taimaka matuƙa wajen kawo ƙarshen matsalolin da suka daɗe suna hana yankin samun ci gaba.

ADVERTISEMENT
  • Shugabar Bulgaria Iliana Yotova: Muna Begen Ganin Kamfanonin Sin Sun Kara Zuba Jari A Kasarmu
  • Yadda Ake Hada Dilka Na Amare

Shettima Yerima ya bayyana hakan ne yayin zantawarsa da manema labarai Jim kadan bayan kammala bude taron. Ya ce taron ya haɗa kowane bangare na al’umma, ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba, domin tsara ingantacciyar hanya ta samun ci gaban tattalin arziki da siyasa a yankin.

 

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

A cewarsa, a matsayinsu na mahalarta taron, sun shirya tsaf domin gabatar da muhimman batutuwan ci gaba da suka shafi farfaɗo da masana’antu da suka durƙushe, rage matsalar rashin tsaro ga rayuka da dukiyoyi, bunƙasa harkar noma ta zama sana’ar dogon lokaci, tare da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai tsakanin kabilu da addinai daban-daban a Arewa baki ɗaya.

 

Honarabul Yerima ya ƙara da cewa shugabannin Arewa, duk da bambancin ra’ayoyin siyasa, za su haɗa kai wajen jagorantar samar da taswirar hanyoyin magance matsaloli da suka daɗe suna hana yankin samun ci gaba a baya, tare da buɗe sabon babi na cin gajiyar dimbin albarkatun ɗan Adam da na ƙasa da yankin ke da su.

 

Ya kuma yi wa mahalarta taron daga jihohi bakwai na Arewa maso Yamma fatan samun tattaunawa mai armashi wadda za ta amfani yankin da ma sauran shiyyoyin ƙasar nan.

 

A ƙarshe, Shettima Yerima ya yi kira ga masu shirya taron hukumar raya Arewa maso yamma (NWDC), Kwamitin Majalisar Dattawa kan Arewa maso Yamma, da gwamnonin jihohi bakwai na yankin da su tabbatar da aiwatar da shawarwarin da aka cimma a taron, domin amfanin al’ummar Arewa maso Yamma baki ɗaya.

Shettima
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
Shettima
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
2027: PDP Za Ta Yi Duk Abin Da Ya Dace Domin Ceto Dimokiraɗiyyar Nijeriya – Jigo A PDP

2027: PDP Za Ta Yi Duk Abin Da Ya Dace Domin Ceto Dimokiraɗiyyar Nijeriya – Jigo A PDP

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.