ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: PDP Za Ta Yi Duk Abin Da Ya Dace Domin Ceto Dimokiraɗiyyar Nijeriya – Jigo A PDP

by Muhammad Bashir
6 months ago
PDP

Mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa mai kula da shiyyar Kudu–Maso-Kudu, Emmanuel Ogidi, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta ɗauki matakai masu ƙarfi domin kare dimokiraɗiyyar Nijeriya, tare da ƙarfafa haɗin kan ƙasa a gabanin zaɓen 2027.

Ogidi ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a ranar Lahadi, inda ya ce PDP na shirin sake tsayawa tsaye a matsayin jam’iyyar adawa mai ƙarfi, wadda za ta iya daidaita tafiyar mulki da kuma kawo ci gaba ga al’ummar ƙasa.

  • Gwamna Lawal Ya Fara Ganawa Da Manyan Jiga-jigan PDP A Zamfara
  • Zamfara: PDP Ta Yaba Wa Kotun Abuja Kan Nasarar Da Ta Samu

Ya amince da cewa jam’iyyar na fuskantar wasu matsaloli na cikin gida, amma ya jaddada cewa waɗannan ƙalubalen ba za su hana PDP cika aikinta na kare dimokiraɗiyya da muradun jama’a ba. A cewarsa, jam’iyyar ba za ta ci amanar ‘yan Nijeriya da ke kallonta a matsayin ginshiƙin adawa a ƙasar nan ba.

ADVERTISEMENT

Jigon na PDP ya ƙara da cewa jam’iyyar za ta buɗe ƙofofin tattaunawa da sauran masu ruwa da tsaki a fagen siyasa, ciki har da wasu daga jam’iyyar APC, domin haɗa kai wajen kare dimokiraɗiyyar ƙasa, inda ya yi gargaɗin cewa sakaci kan wannan batu na iya jefa Nijeriya cikin manyan matsaloli.

A ƙarshe, Ogidi ya ce babban burin PDP a zaɓen 2027 shi ne tabbatar da dimokiraɗiyya mai ƙarfi, ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma inganta tsarin siyasa a faɗin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

PDP
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
A.A. Zaura Ya Wakilci Gwamna Abba Wajen Karɓo Lambar Yabo A Legas

A.A. Zaura Ya Wakilci Gwamna Abba Wajen Karɓo Lambar Yabo A Legas

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da Takardar Matsayinta Kan Shugabancin Intanet A Zamanin Fasahohin Zamani

Sin Ta Fitar Da Takardar Matsayinta Kan Shugabancin Intanet A Zamanin Fasahohin Zamani

July 22, 2026
Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Gina Halaye Nagari Ta Hanyar Ilimi Da Inganta Tsarin Ilimi Na Tushe A Matakin Koli

Shugaba Xi Ya Jaddada Muhimmancin Gina Halaye Nagari Ta Hanyar Ilimi Da Inganta Tsarin Ilimi Na Tushe A Matakin Koli

July 22, 2026
Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.