Wasu mazauna Babban Birnin Tarayya, ciki har da masu saye da ‘yan kasuwa, sun koka cewa hauhawar farashin abinci ta kara tsananta musu rayuwa.
Mazaunan sun bayyana hakan ne a wata tattaunawa da Kamfanin Dillacin Labaran Nijeriya ta yi da su a ranar Lahadi a Abuja.
Wani bincike da NAN ta gudanar a kasuwannin FCT da dama, ciki har da Dei-Dei, Kubwa da Dutse, ya nuna karuwa mai yawa a farashin muhimman kayan abinci.
Sakamakon binciken ya nuna cewa gidaje da dama suna sauya tsarin cin abincinsu, domin hauhawar farashi ya sa ya zama wahala a ci abinci sau uku a rana.
A cewar mazauna, halin da ake ciki ya tilasta musu rage yawan abinci da kuma komawa kan nau’ukan abinci masu araha.
NAN ta kuma ruwaito cewa ‘yan kasuwa sun koka da raguwar ciniki, inda suka danganta hakan da karancin karfin sayen kayayyaki na kwastomomi.
Wani dillalin kayan lambu a kasuwar Dei-Dei, Malam Adamu Isah, ya ce ‘yan kasuwa na fuskantar manyan kalubale sakamakon tsananin tashin farashin abinci da kuma raguwar masu saya.
“Da farko, ana sayar da babban kwandon tumatir tsakanin Naira 18,000 zuwa Naira 25,000, amma yanzu ana sayar da shi tsakanin Naira 45,000 zuwa Naira 48,000.
“Buhun barkono wanda a da ake sayarwa tsakanin Naira 70,000 zuwa Naira 85,000, yanzu ya kai tsakanin Naira 80,000 zuwa Naira 96,000.”
Sai dai Adamu ya nuna damuwa kan asarar kudade sakamakon lalacewar kayan abinci kafin a sayar.
“Wasu lokuta, har kashi daya bisa hudu ko rabin kwandon tumatir na lalacewa kafin a sayar, lamarin da ke janyo asara,” in ji shi.
Ya danganta matsalar da hauhawar farashin man fetur, wanda ke janyo jinkiri wajen kai kayayyaki zuwa kasuwa.
“Jigilar kaya na da matukar muhimmanci a wannan sana’a. Muna sayo kayayyaki daga gonaki, amma muna fuskantar kalubale wajen kawo su kasuwa.
“Muna rokon gwamnati ta magance matsalar farashin mai, domin yana matukar shafar sana’o’inmu da rayuwarmu,” in ji shi.
Wata ‘yar kasuwa a kasuwar Kubwa, Hajiya Peace Dabid, ta kuma koka da raguwar ciniki, inda ta danganta hakan da halin tattalin arzikin kasar.
“A da, ina sayar da karamar robar tumatir tsakanin Naira 1,500 zuwa Naira 1,800, amma yanzu ya kai tsakanin Naira 4,000 zuwa Naira 4,500.
“Karamin kwandon barkono yanzu ya kai Naira 10,000, kusan ninki biyu daga tsohon farashinsa na Naira 5,500 zuwa Naira 6,000.”
Wani mai sayar da hatsi a kasuwar Dutse, Malam Ahmad, ya ce ‘yan kasuwa na kokarin ci gaba da kasuwancinsu duk da kalubalen.
“Muna dai jurewa ne don kada mu tsaya cak, amma sauyin farashi a kai a kai ba abin karfafawa ba ne.
“Mutum ba zai iya tsara gobe ba, domin ba ka san farashin kaya a lokaci mai zuwa ba,” in ji shi.
Ya ce buhun shinkafa mai kilo 50 yanzu ana sayar da shi tsakanin Naira 52,000 zuwa Naira 55,000, sabanin Naira 46,000 zuwa Naira 48,000 da aka samu kimanin watanni biyu da suka gabata.
Ya kara da cewa wake yanzu ya kai tsakanin Naira 80,000 zuwa Naira 82,000 kan buhun kilo 50, daga Naira 69,000 zuwa Naira 72,000 a baya, yayin da guga daya na garri ke sayarwa tsakanin Naira 2,000 zuwa Naira 2,500, daga tsohon farashi na Naira 1,200 zuwa Naira 1,500.
Malam Rabi’u Haruna, mai sayar da sukari a kasuwar Dutse, ya ce tsadar sufuri ta rage musu ribar kasuwanci.
“Yanzu ina sayen sukari a Naira 65,000 maimakon Naira 60,000. Wasu lokuta ma, ko mun sayar ba ma samun riba saboda kudin sufuri.”
Wani mazauni, Malam Paul Ugo, ya ce ci gaba da tashin farashi na shafar masu saya da masu sayarwa baki daya.
“A da, ina saye da yawa, amma yanzu sai kanana-kanana nake iya saya.”
Hajiya Safiya Muhammad, wata mazauniya, ta nuna damuwa kan yadda hauhawar farashin abinci ke shafar gidanta.
“Ciyar da iyalina ya zama da wahala sosai. Yanzu ina rage girki kuma ina mai da hankali kan abinci masu saukin araha domin mu iya jurewa.”
Ta bukaci gwamnati da ta dauki matakan gaggawa domin daidaita farashi da rage wahalar da jama’a ke ciki.
Bayanan Hukumar Kididdiga ta Kasa sun nuna cewa hauhawar farashin abinci a Nijeriya ya kai kashi 14.31 cikin dari a watan Maris na 2026 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, abin da ke nuna ci gaba da matsin lamba kan farashin abinci a fadin kasar.
Binciken ya nuna karuwa da matsin tattalin arziki ga ‘yan kasuwa da masu saye, yayin da kudaden shiga ke nan daram amma farashin abinci ke ci gaba da tashi.















Discussion about this post