Rundunar ‘yansandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane a birnin Ilorin, babban birnin jihar.
Mai magana da yawun rundunar, Adetoun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da kamen a wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar, inda ta ce jami’an sashin kai ɗauki (IRT) sun kama mutanen ne bayan samun sahihan bayanan sirri da kuma sanya ido na musamman.
Ta bayyana cewa waɗanda aka kama sun haɗa da Adamu Ibrahim mai shekara 30 da Sani Musa mai shekara 29, inda bincike na farko ya nuna cewa suna cikin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ke addabar al’ummar jihar.
Sanarwar ta ƙara da cewa domin kaucewa gano su, waɗanda ake zargin sun bai wa wata mace makaman su domin kai su wani wuri da suka shirya gudanar da ayyukan ta’addanci. Bayan tambayoyi, sun jagoranci jami’an tsaro zuwa wata maɓoya inda aka ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda uku, da mujallu guda biyar da harsasai 143.
Rundunar ta ce bincike ya nuna cewa ƙungiyar na shirin kai wani hari ne kafin jami’an tsaro su daƙile shirin ta hanyar amfani da bayanan sirri.
A yanzu haka waɗanda aka kama suna hannun ‘yansanda yayin da ake ci gaba da neman sauran mambobin ƙungiyar kafin gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.















Discussion about this post