ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Bunkasa A 2025 — Minista

by Leadership Hausa
9 months ago

Gwamnatin tarayya ta ce tattalin arzikin Nijeriya na ci gaba da bunkasa a kowane wata na tsawon watanni 12 a jere a shekarar 2025, abin da ke nuna ci gaba mai dorewa a harkokin tattalin arziki duk da kalubale na duniya da na cikin gida.

Ministan Harkokin Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ne ya bayyana wannan a ranar Litinin a Abuja yayin gabatar da rahoton gwamnatinsa na karshen shekara.

  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno
  • Mutane 5 Sun Rasu, 35 Sun Jikkata A Harin Bam A Masallaci A Borno

Idris ya ce wannan ci gaba mai dorewa ya bayyana a cikin (PMI), wani muhimmin ma’auni na amincewar ‘yan kasuwa, wanda ya nuna ci gaba ba tare da katsewa ba a duk shekara.

ADVERTISEMENT

“Bayanan PMI na baya-bayan nan wanda shi ne muhimmin ma’auni na yanayin kasuwanci sun nuna cewa Nijeriya ta samu watanni 12 a jere cikin bunkasar harkokin tattalin arziki,” in ji shi.

Idris ya bayyana cewa wannan nasara ta nuna karfin sashen tattalin arzikin da ba na mai ba, ko da yake akwai matsin lamba daga hauhawar farashi da rashin tabbas na tattalin arzikin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

A cewar ministan, Jimillar Kadarorin Cikin Gida (GDP) na Nijeriya ya karu da kashi 3.98 cikin dari a kwata na uku na shekarar 2025, inda babban abin da ya ja wannan ci gaba shi ne bunkasar ayyuka, kasuwanci da masana’antu.

Ya kuma ce hauhawar farashin kayayyaki ya ragu na tsawon watanni takwas a jere zuwa kashi 14.45 cikin dari a watan Nuwamba 2025, yayin da ajiyar kudin kasa na waje ya karu zuwa kusan Dala biliyan 44.56.

“Ajiyar kudin kasarmu na waje ya karu zuwa kusan Dala biliyan 44.56, wanda ke samar da kariya mai karfi wacce ke daidaita darajar kudinmu kuma ke ba masu zuba jari na kasa da kasa kwarin gwiwa,” in ji shi.

Idris ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ta dage wajen karfafa daidaiton tattalin arziki na kasa baki daya da tabbatar da cewa alamomin ci gaban tattalin arziki su canza zuwa ingantattun rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa kasafin kudin shekarar 2026 zai bai wa tsaro fifiko, ci gaban ababen more rayuwa, karfafa matasa da jin dadin al’umma domin ci gaba da bunkasa tattalin arzikin da ake samu a yanzu.

“Manufar shekarar 2026 ita ce gina tubalin Nijeriya mai tsaro, mai fafatawa da kuma mai wadata,” in ji ministan, yana mai cewa sauye-sauyen da gwamnatin ta aiwatar suna fara haifar da fa’idodi na dogon lokaci.

Ya bayyana hangen nesa na Shugaba Bola Tinubu ga kasa a matsayin mai jarumta da mai mai da hankali, inda ya tabbatar cewa Nijeriya “Da gaske na kan tafiya” zuwa ci gaba mai dorewa da hadin gwiwa.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Labarai

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
AFCON 2026: Salah Ya Kai Masar Zagayen ‘Yan 16

AFCON 2026: Salah Ya Kai Masar Zagayen 'Yan 16

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.