Tattaunawar da aka yi tsakanin Gwamnatin Tarayya da Kwamitin Hadin Gwiwa (JAC) na kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i ta kare ba tare da cimma matsaya ba a ranar Litinin a Abuja, yayin da manyan batutuwa suka ci gaba da zama cikin rashin tabbas dangane da rashin warware su.
JAC ya kunshi Manyan Kungiyoyin Jami’o’in Nijeriya da kuma Kungiyar Ma’aikatan Jami’o’in Da Ba Sa Koyarwa.
An dage taron, wanda Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya kira, zuwa ranar 5 ga Mayu domin ci gaba da tattaunawa.
Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya tunatar da cewa SSANU da NASU sun fara yajin aiki na sai baba-ta-gani a ranar 30 ga Afrilu bayan cikar wa’adin wata guda da suka bai wa gwamnatin tarayya kan sake duba yarjejeniyar shekarar 2009.
Kungiyoyin na nuna adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara albashi da kashi 30 cikin dari, inda suka nace a kan karin kashi 40 cikin dari ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.
Tun da farko, gwamnatin tarayya ta janye tayin karin kashi 30 cikin dari, matakin da kungiyoyin suka bayyana a matsayin na kai-tsaye ba tare da cikakkiyar tattaunawa ba.
Da yake magana kan yajin aikin, Shugaban Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Nijeriya, Mista Mohammed Ibrahim, ya ce an bi umarnin yajin aikin bai-daya a fadin kasar, lamarin da ya gurgunta ayyukan gudanarwa da muhimman hidimomi a jami’o’i.
“Bukatunmu ba su canza ba. Kashi 40 cikin dari shi ne mafi kankantar matsayi da za mu amince da shi, kuma yajin aikin zai ci gaba har sai an samu gagarumin ci gaba,” in ji shi.
Ibrahim ya ce ofisoshin gudanarwa, asibitoci, dakunan kwanan dalibai da sassan kudi sun kulle a jami’o’i daban-daban sakamakon cikakken bin umarnin yajin aikin.
A wani bangaren kuma, Jami’ar of Maiduguri ta dage jarrabawar (e-edams) dinta saboda tangardar da yajin aikin ya haifar.
Haka kuma, yajin aikin ya nakasa harkokin karatu da gudanarwa a Ahmadu Bello Unibersity.
Binciken wakilinmu ya nuna cewa an rufe ginin majalisar jami’a (Senate), dakin karatu da kuma asibitin jami’ar.
Haka zalika, an rufe sassan ayyuka da kula da kadarori, lamarin da ya janyo tangarda ga samar da ruwa da wutar lantarki a jami’ar.
Da yake magana da manema labarai yayin wata zanga-zangar lumana a babban harabar jami’ar, shugaban SSANU reshen ABU, Shuaibu Ahmed Halilu, ya ce sun bi umarnin da kungiyar kasa ta bayar kan yajin aikin.















Discussion about this post