ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattaunawar Gwamnatin Tarayya Da SSANU Da NASU Ta Tashi Baram-baran

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
NASU

Tattaunawar da aka yi tsakanin Gwamnatin Tarayya da Kwamitin Hadin Gwiwa (JAC) na kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i ta kare ba tare da cimma matsaya ba a ranar Litinin a Abuja, yayin da manyan batutuwa suka ci gaba da zama cikin rashin tabbas dangane da rashin warware su.

JAC ya kunshi Manyan Kungiyoyin Jami’o’in Nijeriya da kuma Kungiyar Ma’aikatan Jami’o’in Da Ba Sa Koyarwa.

An dage taron, wanda Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya kira, zuwa ranar 5 ga Mayu domin ci gaba da tattaunawa.

ADVERTISEMENT

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya tunatar da cewa SSANU da NASU sun fara yajin aiki na sai baba-ta-gani a ranar 30 ga Afrilu bayan cikar wa’adin wata guda da suka bai wa gwamnatin tarayya kan sake duba yarjejeniyar shekarar 2009.

Kungiyoyin na nuna adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara albashi da kashi 30 cikin dari, inda suka nace a kan karin kashi 40 cikin dari ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Tun da farko, gwamnatin tarayya ta janye tayin karin kashi 30 cikin dari, matakin da kungiyoyin suka bayyana a matsayin na kai-tsaye ba tare da cikakkiyar tattaunawa ba.

Da yake magana kan yajin aikin, Shugaban Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Nijeriya, Mista Mohammed Ibrahim, ya ce an bi umarnin yajin aikin bai-daya a fadin kasar, lamarin da ya gurgunta ayyukan gudanarwa da muhimman hidimomi a jami’o’i.

“Bukatunmu ba su canza ba. Kashi 40 cikin dari shi ne mafi kankantar matsayi da za mu amince da shi, kuma yajin aikin zai ci gaba har sai an samu gagarumin ci gaba,” in ji shi.

Ibrahim ya ce ofisoshin gudanarwa, asibitoci, dakunan kwanan dalibai da sassan kudi sun kulle a jami’o’i daban-daban sakamakon cikakken bin umarnin yajin aikin.

A wani bangaren kuma, Jami’ar of Maiduguri ta dage jarrabawar (e-edams) dinta saboda tangardar da yajin aikin ya haifar.

Haka kuma, yajin aikin ya nakasa harkokin karatu da gudanarwa a Ahmadu Bello Unibersity.

Binciken wakilinmu ya nuna cewa an rufe ginin majalisar jami’a (Senate), dakin karatu da kuma asibitin jami’ar.

Haka zalika, an rufe sassan ayyuka da kula da kadarori, lamarin da ya janyo tangarda ga samar da ruwa da wutar lantarki a jami’ar.

Da yake magana da manema labarai yayin wata zanga-zangar lumana a babban harabar jami’ar, shugaban SSANU reshen ABU, Shuaibu Ahmed Halilu, ya ce sun bi umarnin da kungiyar kasa ta bayar kan yajin aikin.

NASU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
NASU
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Yobe, Sun Kashe Ƴan Ta’adda 50

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Yobe, Sun Kashe Ƴan Ta’adda 50

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
NASU

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.