ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattaunawar Gwamnatin Tarayya Da SSANU Da NASU Ta Tashi Baram-baran

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
NASU

Tattaunawar da aka yi tsakanin Gwamnatin Tarayya da Kwamitin Hadin Gwiwa (JAC) na kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i ta kare ba tare da cimma matsaya ba a ranar Litinin a Abuja, yayin da manyan batutuwa suka ci gaba da zama cikin rashin tabbas dangane da rashin warware su.

JAC ya kunshi Manyan Kungiyoyin Jami’o’in Nijeriya da kuma Kungiyar Ma’aikatan Jami’o’in Da Ba Sa Koyarwa.

An dage taron, wanda Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya kira, zuwa ranar 5 ga Mayu domin ci gaba da tattaunawa.

ADVERTISEMENT

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya tunatar da cewa SSANU da NASU sun fara yajin aiki na sai baba-ta-gani a ranar 30 ga Afrilu bayan cikar wa’adin wata guda da suka bai wa gwamnatin tarayya kan sake duba yarjejeniyar shekarar 2009.

Kungiyoyin na nuna adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara albashi da kashi 30 cikin dari, inda suka nace a kan karin kashi 40 cikin dari ta hanyar tattaunawa da hadin gwiwa.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Tun da farko, gwamnatin tarayya ta janye tayin karin kashi 30 cikin dari, matakin da kungiyoyin suka bayyana a matsayin na kai-tsaye ba tare da cikakkiyar tattaunawa ba.

Da yake magana kan yajin aikin, Shugaban Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Nijeriya, Mista Mohammed Ibrahim, ya ce an bi umarnin yajin aikin bai-daya a fadin kasar, lamarin da ya gurgunta ayyukan gudanarwa da muhimman hidimomi a jami’o’i.

“Bukatunmu ba su canza ba. Kashi 40 cikin dari shi ne mafi kankantar matsayi da za mu amince da shi, kuma yajin aikin zai ci gaba har sai an samu gagarumin ci gaba,” in ji shi.

Ibrahim ya ce ofisoshin gudanarwa, asibitoci, dakunan kwanan dalibai da sassan kudi sun kulle a jami’o’i daban-daban sakamakon cikakken bin umarnin yajin aikin.

A wani bangaren kuma, Jami’ar of Maiduguri ta dage jarrabawar (e-edams) dinta saboda tangardar da yajin aikin ya haifar.

Haka kuma, yajin aikin ya nakasa harkokin karatu da gudanarwa a Ahmadu Bello Unibersity.

Binciken wakilinmu ya nuna cewa an rufe ginin majalisar jami’a (Senate), dakin karatu da kuma asibitin jami’ar.

Haka zalika, an rufe sassan ayyuka da kula da kadarori, lamarin da ya janyo tangarda ga samar da ruwa da wutar lantarki a jami’ar.

Da yake magana da manema labarai yayin wata zanga-zangar lumana a babban harabar jami’ar, shugaban SSANU reshen ABU, Shuaibu Ahmed Halilu, ya ce sun bi umarnin da kungiyar kasa ta bayar kan yajin aikin.

NASU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
  • Sulaiman
    Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya
  • Sulaiman
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
NASU
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
Manyan Labarai

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Yobe, Sun Kashe Ƴan Ta’adda 50

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Yobe, Sun Kashe Ƴan Ta’adda 50

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.