Dakarun rundunar haɗin gwuiwa ta Operation HAƊIN KAI sun daƙile wani babban hari da mayaƙan ISWAP suka kai shalƙwatar bataliya ta 27 da ke Buni Gari da kuma shingen bincike na Buni Gari a jihar Yobe, inda aka kashe aƙalla ‘yan ta’adda 50.
Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba, ya bayyana a wata sanarwa cewa harin ya fara ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare ranar Juma’a daga sassa daban-daban, amma dakarun sun mayar da Zafafan martani tare da hana maharan kutsawa cikin sansanin.
Ya ce mayaƙan ISWAP sun kai harin ne daga ɓangaren yamma kafin su ƙara turo mayaƙa daga kudu da kudu maso yamma domin kewaye sansanin, amma dakarun sun tsaya tsayin daka tare da amfani da manyan makamai da dabarun yaƙi wajen ragargazar maharan.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sama sun bayar da bayanan sirri da sa ido daga sama, lamarin da ya taimaka wajen kai hare-haren sama kan maharan yayin da suke tserewa. Rundunar ta ce an ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda takwas, bindigogin GPMG guda biyu, makaman RPG, harsasai da kuma wasu abubuwan fashewa na IED.
Sai dai rundunar ta bayyana cewa sojoji biyu sun rasa rayukansu yayin fafatawar, inda ta yaba da jarumtakar su tare da jaddada cewa ana ci gaba da farautar sauran ‘yan ta’addan domin hana su sake haɗuwa ko kai wani hari a yankin.















Discussion about this post