ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Da APC Sun Yi Watsi Da Shirin Atiku Na Dawo Da Tallafin Man Fetur

by Sadiq
7 days ago

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da jam’iyyar APC sun yi watsi da shirin tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, na dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen 2027.

APC ta ce cire tallafin man fetur mataki ne mai tsauri da ya zama dole, wanda ya taimaka wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati zuwa ayyukan more rayuwa, ilimi, tsaro da sauran fannoni.

Da yake magana a wani taron APC a Abuja, Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa, Nentawe Yilwatda, wanda ya wakilci Tinubu, ya ce tattalin arzikin Nijeriya ya samu ci gaba tun bayan fara sauye-sauyen.

ADVERTISEMENT

Ya ce ajiyar kuɗin ƙasar waje ya kai kusan dala biliyan 52.7, yayin da tattalin arziƙin ƙasar ya ƙaru da kashi 4.43 cikin 100 a zango na biyu na shekarar 2026.

Ya kuma ce hauhawar farashi ya ragu zuwa kusan kashi 15.4 cikin 100.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Yilwatda ya ce Arewa ta amfana sosai daga sauye-sauyen ta hanyar manyan ayyuka kamar bututun iskar gas na Ajaokuta-Kaduna-Kano, NELFUND da wasu manyan ayyukan tituna da layin dogo.

Ya ce sauye-sauyen za su samar da damar kasuwanci tsakanin Arewacin Nijeriya da maƙwabtan ƙasashe.

Isa Yuguda, Shugaban Kwamitin Amintattu na APC Professionals Forum, ya ce tsohon tsarin tallafin man fetur cike yake da almundahana, ɓarna da rashin kyakkyawan tsarin gudanarwa.

Ya ce gwamnati ta samu rarar sama da Naira tiriliyan 15 tun bayan cire tallafin, yana mai gargaɗin cewa dawo da shi na iya ƙara matsin lamba kan kuɗaɗen gwamnati.

Yuguda ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su duba manufofi, ayyukan da aka gudanar da kuma hanyoyin da za su iya magance matsaloli a zahiri yayin zaɓen 2027, maimakon dogaro da alƙawuran samun sauƙi na ɗan wani lokaci.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
2027: INEC Ta Musanta Zargin Sauya Sunayen ’Yan Takarar Jam’iyyar NDC

2027: INEC Ta Musanta Zargin Sauya Sunayen ’Yan Takarar Jam'iyyar NDC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.