ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Jaddada Shirin Gwamnatinsa Na Kafa Ƴansandan Jihohi A Nijeriya

by Sani Anwar
4 months ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, a ranar Litinin da ta gabata, ya tabbatar wa Ƴan Nijeriya cewa; ƙasar na fita daga ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro, inda ya bayyana cewa; Nijeriya ta fita daga cikin dazuzzuka. Ya kuma yi alƙawarin cewa, ana ƙoƙarin kafa Ƴansandan jihohi, domin magance tashe-tashen hankula a faɗin ƙasar nan.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne, a lokacin buɗa baki da gwamnonin jihohi da mataimakan gwamnoni biyu da manyan jami’ai a fadar gwamnati da ke Abuja.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci
  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Ya kuma jaddada buƙatar tsayawa tsayin daka da kuma sadaukar da kai ga farfaɗowar wannan ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Sakamakon aiki tuƙuru, shi ne ƙarin aiki, amma muddin muka haɗa kai kuma muka ƙudiri aniyar ceto ƙasar nan, to mafi alherin yana nan tafe.

“Mun fita daga cikin dazuzzuka, mun kuma fita daga cikin duhun rami na rashin tabbas,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

Dangane da rashin tsaro, shugaba Tinubu ya ƙara da cewa; “Ga waɗanda ba su da aikin yi, na yi alƙawarin za mu kafa Ƴansandan jihohi, domin ƙarfafa tsaro a ƙananan hukumominmu.

Ya kuma yi kira da a haɗa kai da sadaukarwa a yayin da musulmai ke gudanar da azumin watan Ramadan, Kirista kuma su ma na yin nasu azumin.

Tinubu ya yaba wa Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, bisa shirin ciyarwa a wannan wata na Ramadan, sannan ya buƙaci a ƙara ƙarfafa gwiwar matasa da kuma ci gaban ƙasa.

“Tsaɓi da sadaukarwa da bangaskiya da juriya da azama, suna da muhimmanci a gare mu, mu yi addu’a tare, mu ƙaunaci juna da kuma hidimta wa Ɗan’adam,” in ji shi.

Har ila yau, ya kuma yaba wa gwamnonin, bisa nasarorin da suka samu, inda ya nuna cewa; an samu fitowar jama’a da dama duk kuwa da gudanar da taron jam’iyyar da kuma gudanar da ayyukan cikin gida.

“Na gode wa Allah a kan abin da muka samu tare, mun ga ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukanmu,” in ji shi, yana mai jaddada buƙatar yaɗa ayyukan ci gaba a faɗin ƙananan hukumomi da kuma jawo hankalin matasa.

An gabatar da addu’o’i a wajen taron daga mabiya addinin kirista da kuma na musulmi daga bakin babban Limamin gidan gwamnati Abdulwaheed (Muslim) da kuma gwamnan Taraba Agbu Kefas (Kirista).

Tun da farko, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar gwamnonin Nijeriya, ya yaba wa Tinubu kan samar da haɗin kan ƙasa a cikin rikicin addini da ƙabilanci.

Ya kuma bayyana taron a matsayin wanda Allah ya albarkace shi, yana mai cewa; ba kasafai ake haɗuwa a irin wannan wata na Ramadan da Azumin kiristoci ba, a ajiye bambance-bambance a gefe.

Uzodinma ya yaba wa shugaban ƙasar kan inganta haɗin gwiwa da gwamnoni da kuma ƙarfafa tallafa wa marasa galihu a lokacin azumi.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da mambobin majalisar ministoci da dama sun halarci taron tare da gwamnonin da suka haɗa da Aleɗ Otti (Abia), Dapo Abiodun (Ogun), Babagana Zulum (Borno), Inuwa Yahaya (Gombe), Ahmed Aliyu (Sokoto), Sheriff Oboreɓwori (Delta), Abdullahi Sule (Nasarawa), Abba Kabir Yusuf (Kano), da sauransu.

 

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Next Post
Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.