ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Jaddada Shirin Gwamnatinsa Na Kafa Ƴansandan Jihohi A Nijeriya

by Sani Anwar
5 months ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, a ranar Litinin da ta gabata, ya tabbatar wa Ƴan Nijeriya cewa; ƙasar na fita daga ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro, inda ya bayyana cewa; Nijeriya ta fita daga cikin dazuzzuka. Ya kuma yi alƙawarin cewa, ana ƙoƙarin kafa Ƴansandan jihohi, domin magance tashe-tashen hankula a faɗin ƙasar nan.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne, a lokacin buɗa baki da gwamnonin jihohi da mataimakan gwamnoni biyu da manyan jami’ai a fadar gwamnati da ke Abuja.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci
  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Ya kuma jaddada buƙatar tsayawa tsayin daka da kuma sadaukar da kai ga farfaɗowar wannan ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Sakamakon aiki tuƙuru, shi ne ƙarin aiki, amma muddin muka haɗa kai kuma muka ƙudiri aniyar ceto ƙasar nan, to mafi alherin yana nan tafe.

“Mun fita daga cikin dazuzzuka, mun kuma fita daga cikin duhun rami na rashin tabbas,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Dangane da rashin tsaro, shugaba Tinubu ya ƙara da cewa; “Ga waɗanda ba su da aikin yi, na yi alƙawarin za mu kafa Ƴansandan jihohi, domin ƙarfafa tsaro a ƙananan hukumominmu.

Ya kuma yi kira da a haɗa kai da sadaukarwa a yayin da musulmai ke gudanar da azumin watan Ramadan, Kirista kuma su ma na yin nasu azumin.

Tinubu ya yaba wa Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, bisa shirin ciyarwa a wannan wata na Ramadan, sannan ya buƙaci a ƙara ƙarfafa gwiwar matasa da kuma ci gaban ƙasa.

“Tsaɓi da sadaukarwa da bangaskiya da juriya da azama, suna da muhimmanci a gare mu, mu yi addu’a tare, mu ƙaunaci juna da kuma hidimta wa Ɗan’adam,” in ji shi.

Har ila yau, ya kuma yaba wa gwamnonin, bisa nasarorin da suka samu, inda ya nuna cewa; an samu fitowar jama’a da dama duk kuwa da gudanar da taron jam’iyyar da kuma gudanar da ayyukan cikin gida.

“Na gode wa Allah a kan abin da muka samu tare, mun ga ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukanmu,” in ji shi, yana mai jaddada buƙatar yaɗa ayyukan ci gaba a faɗin ƙananan hukumomi da kuma jawo hankalin matasa.

An gabatar da addu’o’i a wajen taron daga mabiya addinin kirista da kuma na musulmi daga bakin babban Limamin gidan gwamnati Abdulwaheed (Muslim) da kuma gwamnan Taraba Agbu Kefas (Kirista).

Tun da farko, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar gwamnonin Nijeriya, ya yaba wa Tinubu kan samar da haɗin kan ƙasa a cikin rikicin addini da ƙabilanci.

Ya kuma bayyana taron a matsayin wanda Allah ya albarkace shi, yana mai cewa; ba kasafai ake haɗuwa a irin wannan wata na Ramadan da Azumin kiristoci ba, a ajiye bambance-bambance a gefe.

Uzodinma ya yaba wa shugaban ƙasar kan inganta haɗin gwiwa da gwamnoni da kuma ƙarfafa tallafa wa marasa galihu a lokacin azumi.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da mambobin majalisar ministoci da dama sun halarci taron tare da gwamnonin da suka haɗa da Aleɗ Otti (Abia), Dapo Abiodun (Ogun), Babagana Zulum (Borno), Inuwa Yahaya (Gombe), Ahmed Aliyu (Sokoto), Sheriff Oboreɓwori (Delta), Abdullahi Sule (Nasarawa), Abba Kabir Yusuf (Kano), da sauransu.

 

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.