ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Jaddada Shirin Gwamnatinsa Na Kafa Ƴansandan Jihohi A Nijeriya

by Sani Anwar
6 months ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, a ranar Litinin da ta gabata, ya tabbatar wa Ƴan Nijeriya cewa; ƙasar na fita daga ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro, inda ya bayyana cewa; Nijeriya ta fita daga cikin dazuzzuka. Ya kuma yi alƙawarin cewa, ana ƙoƙarin kafa Ƴansandan jihohi, domin magance tashe-tashen hankula a faɗin ƙasar nan.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne, a lokacin buɗa baki da gwamnonin jihohi da mataimakan gwamnoni biyu da manyan jami’ai a fadar gwamnati da ke Abuja.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci
  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Ya kuma jaddada buƙatar tsayawa tsayin daka da kuma sadaukar da kai ga farfaɗowar wannan ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Sakamakon aiki tuƙuru, shi ne ƙarin aiki, amma muddin muka haɗa kai kuma muka ƙudiri aniyar ceto ƙasar nan, to mafi alherin yana nan tafe.

“Mun fita daga cikin dazuzzuka, mun kuma fita daga cikin duhun rami na rashin tabbas,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Dangane da rashin tsaro, shugaba Tinubu ya ƙara da cewa; “Ga waɗanda ba su da aikin yi, na yi alƙawarin za mu kafa Ƴansandan jihohi, domin ƙarfafa tsaro a ƙananan hukumominmu.

Ya kuma yi kira da a haɗa kai da sadaukarwa a yayin da musulmai ke gudanar da azumin watan Ramadan, Kirista kuma su ma na yin nasu azumin.

Tinubu ya yaba wa Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, bisa shirin ciyarwa a wannan wata na Ramadan, sannan ya buƙaci a ƙara ƙarfafa gwiwar matasa da kuma ci gaban ƙasa.

“Tsaɓi da sadaukarwa da bangaskiya da juriya da azama, suna da muhimmanci a gare mu, mu yi addu’a tare, mu ƙaunaci juna da kuma hidimta wa Ɗan’adam,” in ji shi.

Har ila yau, ya kuma yaba wa gwamnonin, bisa nasarorin da suka samu, inda ya nuna cewa; an samu fitowar jama’a da dama duk kuwa da gudanar da taron jam’iyyar da kuma gudanar da ayyukan cikin gida.

“Na gode wa Allah a kan abin da muka samu tare, mun ga ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukanmu,” in ji shi, yana mai jaddada buƙatar yaɗa ayyukan ci gaba a faɗin ƙananan hukumomi da kuma jawo hankalin matasa.

An gabatar da addu’o’i a wajen taron daga mabiya addinin kirista da kuma na musulmi daga bakin babban Limamin gidan gwamnati Abdulwaheed (Muslim) da kuma gwamnan Taraba Agbu Kefas (Kirista).

Tun da farko, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar gwamnonin Nijeriya, ya yaba wa Tinubu kan samar da haɗin kan ƙasa a cikin rikicin addini da ƙabilanci.

Ya kuma bayyana taron a matsayin wanda Allah ya albarkace shi, yana mai cewa; ba kasafai ake haɗuwa a irin wannan wata na Ramadan da Azumin kiristoci ba, a ajiye bambance-bambance a gefe.

Uzodinma ya yaba wa shugaban ƙasar kan inganta haɗin gwiwa da gwamnoni da kuma ƙarfafa tallafa wa marasa galihu a lokacin azumi.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da mambobin majalisar ministoci da dama sun halarci taron tare da gwamnonin da suka haɗa da Aleɗ Otti (Abia), Dapo Abiodun (Ogun), Babagana Zulum (Borno), Inuwa Yahaya (Gombe), Ahmed Aliyu (Sokoto), Sheriff Oboreɓwori (Delta), Abdullahi Sule (Nasarawa), Abba Kabir Yusuf (Kano), da sauransu.

 

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.