ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Jaddada Shirin Gwamnatinsa Na Kafa Ƴansandan Jihohi A Nijeriya

by Sani Anwar
3 months ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, a ranar Litinin da ta gabata, ya tabbatar wa Ƴan Nijeriya cewa; ƙasar na fita daga ƙalubalen tattalin arziƙi da tsaro, inda ya bayyana cewa; Nijeriya ta fita daga cikin dazuzzuka. Ya kuma yi alƙawarin cewa, ana ƙoƙarin kafa Ƴansandan jihohi, domin magance tashe-tashen hankula a faɗin ƙasar nan.

Shugaban ya yi wannan jawabi ne, a lokacin buɗa baki da gwamnonin jihohi da mataimakan gwamnoni biyu da manyan jami’ai a fadar gwamnati da ke Abuja.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci
  • Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Ya kuma jaddada buƙatar tsayawa tsayin daka da kuma sadaukar da kai ga farfaɗowar wannan ƙasa.

ADVERTISEMENT

“Sakamakon aiki tuƙuru, shi ne ƙarin aiki, amma muddin muka haɗa kai kuma muka ƙudiri aniyar ceto ƙasar nan, to mafi alherin yana nan tafe.

“Mun fita daga cikin dazuzzuka, mun kuma fita daga cikin duhun rami na rashin tabbas,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Dangane da rashin tsaro, shugaba Tinubu ya ƙara da cewa; “Ga waɗanda ba su da aikin yi, na yi alƙawarin za mu kafa Ƴansandan jihohi, domin ƙarfafa tsaro a ƙananan hukumominmu.

Ya kuma yi kira da a haɗa kai da sadaukarwa a yayin da musulmai ke gudanar da azumin watan Ramadan, Kirista kuma su ma na yin nasu azumin.

Tinubu ya yaba wa Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, bisa shirin ciyarwa a wannan wata na Ramadan, sannan ya buƙaci a ƙara ƙarfafa gwiwar matasa da kuma ci gaban ƙasa.

“Tsaɓi da sadaukarwa da bangaskiya da juriya da azama, suna da muhimmanci a gare mu, mu yi addu’a tare, mu ƙaunaci juna da kuma hidimta wa Ɗan’adam,” in ji shi.

Har ila yau, ya kuma yaba wa gwamnonin, bisa nasarorin da suka samu, inda ya nuna cewa; an samu fitowar jama’a da dama duk kuwa da gudanar da taron jam’iyyar da kuma gudanar da ayyukan cikin gida.

“Na gode wa Allah a kan abin da muka samu tare, mun ga ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukanmu,” in ji shi, yana mai jaddada buƙatar yaɗa ayyukan ci gaba a faɗin ƙananan hukumomi da kuma jawo hankalin matasa.

An gabatar da addu’o’i a wajen taron daga mabiya addinin kirista da kuma na musulmi daga bakin babban Limamin gidan gwamnati Abdulwaheed (Muslim) da kuma gwamnan Taraba Agbu Kefas (Kirista).

Tun da farko, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar gwamnonin Nijeriya, ya yaba wa Tinubu kan samar da haɗin kan ƙasa a cikin rikicin addini da ƙabilanci.

Ya kuma bayyana taron a matsayin wanda Allah ya albarkace shi, yana mai cewa; ba kasafai ake haɗuwa a irin wannan wata na Ramadan da Azumin kiristoci ba, a ajiye bambance-bambance a gefe.

Uzodinma ya yaba wa shugaban ƙasar kan inganta haɗin gwiwa da gwamnoni da kuma ƙarfafa tallafa wa marasa galihu a lokacin azumi.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila da mambobin majalisar ministoci da dama sun halarci taron tare da gwamnonin da suka haɗa da Aleɗ Otti (Abia), Dapo Abiodun (Ogun), Babagana Zulum (Borno), Inuwa Yahaya (Gombe), Ahmed Aliyu (Sokoto), Sheriff Oboreɓwori (Delta), Abdullahi Sule (Nasarawa), Abba Kabir Yusuf (Kano), da sauransu.

 

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.