ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci

by Sani Anwar
4 months ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya buƙaci gwamnatin tarayya, ta gaggauta shiga tsakani tare da ƙarfafa tallafin tsaro, biyo bayan wani ƙazamin hari da Ƴan bindiga suka kai a yankin Kafin Duguri, inda aka kashe mazauna garin tare da jikkata wasu.

Gwamnan, ya yi wannan roƙo ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa al’umma, inda ya bayyana harin a matsayin wani babban ƙalubalen tsaro da ya mamaye cibiyoyin tsaro na yankin.

Ya ƙara da cewa, hukumomin tsaro a ƙasa suna buƙatar ƙarin nagartattun makamai da tallafin kayan aiki, domin tunkarar Ƴanbindigar da suka mamaye sassan yankin.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Haifar Da Abubuwan Bakin Cikin Da Ke Faruwa A Minneapolis
  • Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

Gwamna Mohammed ya bayyana cewa, yayin da yake wata ziyarar aiki a Abuja, ya yi wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayanin halin da ake ciki. A cewarsa, shugaban ƙasar a matsayinsa na babban kwamandan sojojin ƙasar, ya jajantawa iyalan waɗanda lamarin ya shafa tare da tabbatar wa al’ummar ƙasar goyon bayan gwamnatin tarayya, domin dawo da zaman lafiya.

Da yake yaba wa wannan bajinta ta mazauna Kafin Duguri, gwamnan ya ce; mutanen sun nuna jajircewar da ba a saba gani ba, musamman wajen tunkarar harin, lamarin da ya tilasta wa maharan ja da baya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; duk da cewa, an yi asarar rayuka da jikkata wasu daga cikin mazauna yankin, amma tsayin-dakan da al’ummar yankin suka yi, ya nuna matuƙar haɗin kai da tsayin daka da kuma kishin ƙasa ga kakanninsu.

Mohammed ya bayyana cewa, an daƙile ayyukan Ƴan bindiga a wasu sassan jihar da suka haɗa da Ƙananan Hukumomin Ningi da Jama’are da kuma Bogoro, amma ya bayyana ci gaba da kai hare-hare a yankinsa na Duguri a matsayin abu maras daɗi.

Ya kuma bai wa mazauna jihar tabbacin cewa, gwamnati ta ɗauki aniyar kawar da masu aikata laifuka gaba-ɗaya a faɗin jihar.

Da yake yin ƙarin haske kan muhimmancin tattalin arziƙin yankin, gwamnan ya ce; Kafin Duguri, yana da arziƙin ƙasa mai albarka da amfanin gona da kuma albarkatun ƙasa, yana mai jaddada cewa; mazauna yankin sun dogara ne da noma sosai, domin rayuwarsu.

Ya ƙara da cewa, ayyukan samar da ababen more rayuwa da ake ci gaba da yi da suka haɗa da gina tituna da ke haɗa al’umma da yankunan da ke maƙwabtaka da su, za su ci gaba da ci gaba duk da ƙalubalen tsaron da ake da shi.

A wani mataki na ɗaukar matakan gaggawa, Gwamna Mohammed ya bayyana shirin ɗaukar sabbin Ƴan banga da kuma horar da su tare da haɗin gwiwar Ƴansanda.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ɗauki cikakken alhakin kula da waɗanda suka jikkata, yayin da aka gudanar da addu’o’in samun rahama ga waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

Bauchi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.