ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci

by Sani Anwar
6 months ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya buƙaci gwamnatin tarayya, ta gaggauta shiga tsakani tare da ƙarfafa tallafin tsaro, biyo bayan wani ƙazamin hari da Ƴan bindiga suka kai a yankin Kafin Duguri, inda aka kashe mazauna garin tare da jikkata wasu.

Gwamnan, ya yi wannan roƙo ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa al’umma, inda ya bayyana harin a matsayin wani babban ƙalubalen tsaro da ya mamaye cibiyoyin tsaro na yankin.

Ya ƙara da cewa, hukumomin tsaro a ƙasa suna buƙatar ƙarin nagartattun makamai da tallafin kayan aiki, domin tunkarar Ƴanbindigar da suka mamaye sassan yankin.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Haifar Da Abubuwan Bakin Cikin Da Ke Faruwa A Minneapolis
  • Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

Gwamna Mohammed ya bayyana cewa, yayin da yake wata ziyarar aiki a Abuja, ya yi wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayanin halin da ake ciki. A cewarsa, shugaban ƙasar a matsayinsa na babban kwamandan sojojin ƙasar, ya jajantawa iyalan waɗanda lamarin ya shafa tare da tabbatar wa al’ummar ƙasar goyon bayan gwamnatin tarayya, domin dawo da zaman lafiya.

Da yake yaba wa wannan bajinta ta mazauna Kafin Duguri, gwamnan ya ce; mutanen sun nuna jajircewar da ba a saba gani ba, musamman wajen tunkarar harin, lamarin da ya tilasta wa maharan ja da baya.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; duk da cewa, an yi asarar rayuka da jikkata wasu daga cikin mazauna yankin, amma tsayin-dakan da al’ummar yankin suka yi, ya nuna matuƙar haɗin kai da tsayin daka da kuma kishin ƙasa ga kakanninsu.

Mohammed ya bayyana cewa, an daƙile ayyukan Ƴan bindiga a wasu sassan jihar da suka haɗa da Ƙananan Hukumomin Ningi da Jama’are da kuma Bogoro, amma ya bayyana ci gaba da kai hare-hare a yankinsa na Duguri a matsayin abu maras daɗi.

Ya kuma bai wa mazauna jihar tabbacin cewa, gwamnati ta ɗauki aniyar kawar da masu aikata laifuka gaba-ɗaya a faɗin jihar.

Da yake yin ƙarin haske kan muhimmancin tattalin arziƙin yankin, gwamnan ya ce; Kafin Duguri, yana da arziƙin ƙasa mai albarka da amfanin gona da kuma albarkatun ƙasa, yana mai jaddada cewa; mazauna yankin sun dogara ne da noma sosai, domin rayuwarsu.

Ya ƙara da cewa, ayyukan samar da ababen more rayuwa da ake ci gaba da yi da suka haɗa da gina tituna da ke haɗa al’umma da yankunan da ke maƙwabtaka da su, za su ci gaba da ci gaba duk da ƙalubalen tsaron da ake da shi.

A wani mataki na ɗaukar matakan gaggawa, Gwamna Mohammed ya bayyana shirin ɗaukar sabbin Ƴan banga da kuma horar da su tare da haɗin gwiwar Ƴansanda.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ɗauki cikakken alhakin kula da waɗanda suka jikkata, yayin da aka gudanar da addu’o’in samun rahama ga waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

Bauchi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post
Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.