ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Nemi Agajin Tinubu Game Da Yaƙi Da Ta’addanci

by Sani Anwar
3 months ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya buƙaci gwamnatin tarayya, ta gaggauta shiga tsakani tare da ƙarfafa tallafin tsaro, biyo bayan wani ƙazamin hari da Ƴan bindiga suka kai a yankin Kafin Duguri, inda aka kashe mazauna garin tare da jikkata wasu.

Gwamnan, ya yi wannan roƙo ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa al’umma, inda ya bayyana harin a matsayin wani babban ƙalubalen tsaro da ya mamaye cibiyoyin tsaro na yankin.

Ya ƙara da cewa, hukumomin tsaro a ƙasa suna buƙatar ƙarin nagartattun makamai da tallafin kayan aiki, domin tunkarar Ƴanbindigar da suka mamaye sassan yankin.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Haifar Da Abubuwan Bakin Cikin Da Ke Faruwa A Minneapolis
  • Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

Gwamna Mohammed ya bayyana cewa, yayin da yake wata ziyarar aiki a Abuja, ya yi wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayanin halin da ake ciki. A cewarsa, shugaban ƙasar a matsayinsa na babban kwamandan sojojin ƙasar, ya jajantawa iyalan waɗanda lamarin ya shafa tare da tabbatar wa al’ummar ƙasar goyon bayan gwamnatin tarayya, domin dawo da zaman lafiya.

Da yake yaba wa wannan bajinta ta mazauna Kafin Duguri, gwamnan ya ce; mutanen sun nuna jajircewar da ba a saba gani ba, musamman wajen tunkarar harin, lamarin da ya tilasta wa maharan ja da baya.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; duk da cewa, an yi asarar rayuka da jikkata wasu daga cikin mazauna yankin, amma tsayin-dakan da al’ummar yankin suka yi, ya nuna matuƙar haɗin kai da tsayin daka da kuma kishin ƙasa ga kakanninsu.

Mohammed ya bayyana cewa, an daƙile ayyukan Ƴan bindiga a wasu sassan jihar da suka haɗa da Ƙananan Hukumomin Ningi da Jama’are da kuma Bogoro, amma ya bayyana ci gaba da kai hare-hare a yankinsa na Duguri a matsayin abu maras daɗi.

Ya kuma bai wa mazauna jihar tabbacin cewa, gwamnati ta ɗauki aniyar kawar da masu aikata laifuka gaba-ɗaya a faɗin jihar.

Da yake yin ƙarin haske kan muhimmancin tattalin arziƙin yankin, gwamnan ya ce; Kafin Duguri, yana da arziƙin ƙasa mai albarka da amfanin gona da kuma albarkatun ƙasa, yana mai jaddada cewa; mazauna yankin sun dogara ne da noma sosai, domin rayuwarsu.

Ya ƙara da cewa, ayyukan samar da ababen more rayuwa da ake ci gaba da yi da suka haɗa da gina tituna da ke haɗa al’umma da yankunan da ke maƙwabtaka da su, za su ci gaba da ci gaba duk da ƙalubalen tsaron da ake da shi.

A wani mataki na ɗaukar matakan gaggawa, Gwamna Mohammed ya bayyana shirin ɗaukar sabbin Ƴan banga da kuma horar da su tare da haɗin gwiwar Ƴansanda.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa, Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ɗauki cikakken alhakin kula da waɗanda suka jikkata, yayin da aka gudanar da addu’o’in samun rahama ga waɗanda suka rasa rayukansu a harin.

Bauchi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

Wane Ne Tunji Disu Sabon Sufeto Janar Na Ƴansanda?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.