ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Shirin Aikin Noma Domin Samar Da Wadataccen Abinci

by Abubakar Abba
4 months ago
Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kaddamar da babban sabon aikin noma na zamani da zummar kara samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Har ila yau, shirin ya kunshi rabar da kayan aikin noma na zamani daidai har guda 9,022, wadanda suka hada da Taraktocin noma, kayan Haro, kayan yin girbin amfanin gona da kuma sauran wasu kayan aikin noma.

  • Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan ISWAP 20 A Jihar Yobe
  • Kudaden Shiga Na Masana’Antun Kimiya Da Fasaha Na Kasar Sin Ya Karu Da 16.1% a Watannin Janairu Da Fabrairun Wannan Shekara

“Muna daukar kasar nan a matsayin daya daga cikin kasashen da suka mayar da hankali wajen aikin noma a fadin duniya, domin muna fitar da ingantaccen amfanin gona zuwa kasuwannin daban-daban a duniya tare kuma da tabbatar da kowane dan Nijeriya ya samu abinci mai gina jiki,” in ji Tinubu.

ADVERTISEMENT

“Muna tunkaho da abin da muke ci gaba da yi, domin wannan kokarin na daga cikin alkawuranmu na yakin neman zabe da muke burin cika wa al’ummar wannan kasa.”

Tinubu ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ta dauki fannin aikin noma da matukar muhimmanci, domin fannni ne da ke samar da wadataccen abinci ga ‘yan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

“Wannan aiki ne, wanda za a iya cewa; tamkar a yanzu ne muka fara dora damba a kansa”, a cewar shugaban.

Haka zalika, shugaban ya kuma sanar da wadanda suka halaccin taron kaddamar da shirin  tabbacin cewa; wadannan ayyuka na noman zamani, za su kara taimakawa wajen kara samar da ayyuka a fannin aikin noma sama da 2,000.

Ya ci gaba da cewa, kayan za su kuma taimaka wajen kara ayyukan masana’antun kasar da samar da damar gudanar da yin bita da kuma kwararrun kayan aikin noma 9,000.

Shugaban ya jaddada muhimmancin yin amfani da kayan aikin noma na zamani, wanda hakan zai taimaka wa manoman wannan kasa.

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; kaddamar da wannan shiri, wanda yake daidai da na aikin noma a duniya, hakan zai kara bunkasa aikin noman kasar da samar da wadataccen abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

“Ina so mu dauki wannan rana ta kaddamar da wannan shiri tamkar ranar farko ce da Nijeriya ta yunkuro, domin farfado da wannan fanni na aikin noma,“ in ji Tinubu.

“Yin noma da kayan aiki na zamani, shi ne kadai zai iya mayar da manoma tamkar wasu manyan jarumai,” a cewar shugaban.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, wannan shiri; an yi shi ne bisa hadaka da gwamnatin tarayya da kuma kamfanin da ke kera kayan aikin noma na zamani da aka fi sani da ‘APRE BNCC’.

Shi ma, babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa; shirin ya kara tabbatar da yunkurin gwamnatin tarayya, wajen kara habaka fannin aikin noma na kasar, wanda kuma shi ne babban ginshikin ciyar da ta tattalin arzikin kasar gaba.

“Taron na yau da ka kaddamar, ba wai kawai shiri ne don mu ba, illa kawai wata manufa ce ta gwamnatin tarayya na cimma kudurin habaka fannin aikin noman kasar,“ in ji Kyari.

“Ana sa ran za a gudanar da shirin ne, a hekt sama da 550,000 tare da kuma da samar da sama da tan miliyan biyu na hatsi, inda kuma shirin zai samar da ayyukan yi sama da 16,000, wanda kuma sama da ‘yan cirani 560,000 da ke shiyoyi shida na kasar nan, za su amfana, a cewar Ministan.”

Kazalika, Kyari ya bayyana cewa; shirin ya kuma hada da samar da ingantattun Taraktocin noma 2,000, da kayan haro da na fanfunan ban ruwa masu feshi da kayan girbi da sauran makamantansu.

“Mun tanadi sama da na’urori masu kwakwalwa guda 9,000 da kuma kayan gyaransu guda  9,000,” in ji Ministan.

Shi kuwa, a nasa jawabin a wajen taron; Mataimakin Fira Ministan Jamhuriyar Belarus, Bictor Karankebich, ya nuna jin dadinsa kan wannan yarjejeniyar da Nijeriya ta kulla da kasarsa.

Ya bayyana cewa, Jamhuriyar ta Belarus, tana da dogon tarihi wajen kera kayan aikin noma, musamman duba da cewa; kasar ta tura kayan aikin noma da ta kera zuwa sama da kasashe 100 da ke fadin duniya.

Ya ce, shirin wanda ya kasance kashi na farko; ya jaddada muhimmancin bukatar kara hada guiwa, domin wanzar da kashi na biyu na shirin a kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, kashin na wannan shiri, ya hada da samar da cibiyoyin hada Taraktocin noman da sauran kayan aikin noma da kuma bai wa manoma horo, domin sanin yadda za su sarrafa kayan aikin noman, wadanda akasarin kayan na zamani ne.

Idan za a iya tunawa, Majalisar Zartarwa ta Kasa a watan Agustan shekarar 2024 ne, ta amince da yarjejeniya a tsakanin Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci da kuma Jamhuriyar ta Belarus.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
Amurka Ce Tushen Matsalar Da Ake Ciki Dangane Da Batun Nukiliyar Iran

Amurka Ce Tushen Matsalar Da Ake Ciki Dangane Da Batun Nukiliyar Iran

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.