Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa sabon Kwamitin Yaƙin Neman Zaben Shugaban Kasa na jam’iyyar APC gabanin zaɓen shekarar 2027, inda ya naɗa tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, a matsayin Darakta-Janar na kwamitin. Haka zalika, an naɗa Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, a matsayin Sakataren kwamitin yaƙin neman zaben.
Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ta nuna cewa Shugaba Tinubu ne zai kasance shugaban kwamitin (Chairman), yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima da kuma Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda za su kasance mataimakan shugaban kwamitin. Shugaba Tinubu zai yi aiki kafa-da-kafa da wani rukunin masu ba da shawara da suka haɗa da Cif Bisi Akande, Cif Segun Osoba, Sanata Rochas Okorocha, Sanata Abdullahi Adamu, da kuma Sanata Florence Ita Giwa.
Sanarwar ta ƙara da cewa an zabi Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abass, da Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, a matsayin Mataimakan Darakta-Janar domin gudanar da yaƙin neman zaɓen a shiyyoyin Kudu da kuma Arewa. Sanata Adams Oshiomhole zai yi aiki a matsayin mataimakin darakta-janar mai kula da tattaro kan jama’a (mobilisation), yayin da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa (Chief of Staff) zai zama mataimakin darakta-janar mai kula da harkokin gudanarwa.
Haka kuma an sake naɗa James Abiodun Faleke a matsayin mataimakin darakta-janar mai kula da tsare-tsare, sa-ido, da bin kadin zabe, inda zai yi aiki tare da daraktocin shiyyoyi na faɗin ƙasar nan.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Ƙasa, Mohammed Idris Malagi, shi ne aka dora wa alhakin zama daraktan tsare-tsare da yaɗa labarai.
Daga ƙarshe, Shugaba Tinubu ya umarci ɗaukacin mambobin kwamitin da su tashi tsaye haikan domin ganin jam’iyyar APC ta samu gagarumar nasara a zaɓen na watan Janairun 2027, inda ya buƙaci shugabannin ɓangarorin daban-daban da su jawo sauran mambobin jam’iyyar da ba a sanya sunayensu a cikin jerin sunayen kwamitin ba don su bada tasu gudunmawar.














