Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zai kammala wa’adin mulkinsa na shekaru takwas kamar yadda tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya yi.
Onanuga ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani kan muhawarar da ke gudana dangane da tsarin rabon mulki (zoning) da kuma zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.
2027: Batun Murabus Din Masu Rike Da Mukaman Gwamnati
2027: El-Rufai Ya Nesanta Kansa Daga Neman Muƙamin Siyasa
Ya ce, tun da Buhari ya kammala wa’adinsa na shekaru takwas a mulki, ya kamata a bar Tinubu ma ya kammala nasa wa’adin, yana mai jaddada cewa har yanzu yankin Kudu ne ya kamata ya ci gaba da riƙe shugabancin ƙasa zuwa shekarar 2031.
Haka kuma, ya soki wasu ‘yan siyasa, musamman tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, kan kalamansu game da tsarin rabon mulki, yana mai cewa irin waɗannan ra’ayoyi na iya tayar da rikici a tsarin siyasar ƙasa.
Onanuga ya ƙara da cewa tsarin rabon mulki wata hanya ce da ke taimakawa wajen tabbatar da daidaito da haɗin kai tsakanin yankuna, don haka bai kamata a yi watsi da shi ba.A cewarsa, ƙoƙarin kauce wa wannan tsari na iya haddasa rashin jituwa a siyasar Nijeriya.















Discussion about this post