ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Na Son Karbe Ikon Gaza Domin Sauya Wa Falasdinawa Matsuguni

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 year ago
Gaza

Donald Trump ya firgita Falasdinawa kan shawarwarinsa game da makomar zirin Gaza, saboda ya ce Amurka za ta kwace iko da zirin tare sauya fasalinsa.

Wannan ne sauyi mafi girma game da manufofin Amurka kan yankin gabas ta tsakiya cikin gomman shekaru.

  • Thomas Bach Ya Bai Wa Cmg Izinin Sarrafa Watsa Labarun Gasar Olympics Ta Lokacin Hunturu Ta Milan Ta 2026
  • A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

Trump ya bayyana hakan ne a taron manema labarai a fadar White House tare da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu.

ADVERTISEMENT

“Amurka za ta karbi ikon zirin Gaza kuma za mu mallake zirin kuma mu dauki alhalin kwance nakiyoyin da aka dąsa sannan kuma gyara wuraren da aka lalata,” in ji Trump.

Nan da nan firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya nuna jin dadinsa ga kalaman na Mr Trump, inda ya ce hakan zai canza tarihi.

LABARAI MASU NASABA

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

Netanyahu ya ce “Ina kara maimaitawa, muradinmu uku ne kuma na uku shi ne tabbatar da cewa zirin Gaza bai kara zama barazana ga Isra’ila ba.”

Shugaban Amurkar ya kuma bayyana abin da yake tunani game da makomar gabar yamma da kogin Jordan, inda ya ce yana tunanin nuna goyon bayansa ga shirin Isra’ila na kwace iko da gabar yamma din.

Netanyahu dai shi ne shugaban wata kasa na farko da ya kai ziyara fadar White House tun da Trump ya koma kan karagar mulki a karo na biyu.

Abin da Trump ya fada kan kwace Gaza

“Amurka za ta karbe zirrin Gaza, kuma za mu yi abin da ya dace. Za mu mallake shi kuma za mu dau nauyin tsaftace zirrin da lalata duk wasu abubuwan fashewa masu hadari da bama-bamai da ba su fashe ba, da sauran makamai.

“Za mu daidaita komai da kau da gidajen da aka ruguza. Za mu share birnin da samar da ci gaba na tattalin arziki da zai samar da ayyuka mara iyaka da gidaje ga mutanen yankin.

“Za mu yi aiki na gaskiya. Za mu yi abubuwa na daban. Babu koma wa baya. Koma wa baya na nufin a sake fadawa gidan jiya irin yanayin da ake ciki shekaru 100 baya.”

Bayan wadannan kalamai, An yi wa Trump tambayar cewa wane irin iko yake da shi na raba mutane miliyan 1.8 da Gaza.

Martaninsa: “Na hango mun mallake wannan wuri, sannan na hango yadda hakan zai tabbatar da zaman lafiya a wannan yanki na gabas ta tsakiya, babu mamaki baki daya Gabas Ta Tsakiya ma, kuma duk wanda na yi magana da shi, ya fahimci hakan ne mafita.

“Duk mutanen da na tattauna da su, sun nuna goyon-baya da wannan shawara ta Amurka na mallake zirrin, samar da cigaba da ayyuka ga dubbai, tsari ne da ba a taba ganin irinsa ba.”

Me Trump ya ce kan sake tsugunar da al’ummar da ke Gaza a yanzu?

Kafin a shiga taron manema labarai, Trump ya tattauna da Netanyahu a gaban manema labarai a Fadar White House, inda ya yi wadannan kalamai:

“Idan aka yi waiwaye, kullum mutuwa ake yi. Abu ne da an shafe shekaru yana faruwa, kullum mutuwa. Idan muka samu wuri mai kyau da za mu tsugunar da mutanen na dindindin a gidaje masu kyau, inda za su yi rayuwa cikin farin ciki, babu batun harbi ko kashe su, babu batun kashe su da wuka kamar abin da ake gani a Gaza…

“Ina ganin babu laifi sake tsugunar da su, kuma ina ganin za mu cimma hakan a yankunan da shugabannin ke cewa A’a.”

Me Trump ya ke cewa kan mafita da yanayin da Gaza zai kasance?

A karshen taron manema labaran, Trump ya ambato muradansa kan yanayin da Gaza zai kasance nan gaba:

“Har na hango mutane na rayuwa a can, mutane daga sassa na duniya. Ina ganin za mu mayar da zirrin wani yanki da duniya ta jima ba ta gani ba. Gaza wuri ne da ke da dimbin albarkatu.

“Ina ganin duk duniya – wakilai daga ko ina a duniya – za su kasance a can, su ma Falasdinawa za su zauna acan, mutane da dama za su zauna a can…

“Dole mu koyi da abubuwa daga tarihi, ba za mu bari tarihi ya ci gaba da maimaita kansa ba. Muna da damar yin abubuwa na daban.

“Za mu tabbatar mun yi abin da zai kai kololuwa a duniya, zai kayyatar da mutane, Falasdinawa musamman da ake magana a kansu. Duk da dai suna nuna adawa, ina da yakinin cewa Sarkin Jordan da kuma Kasar Masar za su bude mana zuciyarsu da bamu irin yankin da muke so, saboda tabbatuwar burinmu, mutane su yi rayuwa cikin hadin-kai da annushuwa.”

Hamas ta yi tir da Trump

Jim kadan bayan Trump ya kammalan wadannan jawabai na sa ga ‘yan jarida – daya daga cikin jagororin Hamas, Sami Abu Zuhuri ya ce wadannan shawarwari na Trump shirme ya ke yi kuma sun yi tir da hakan.

Ya bayyana matakin da shirin haifar da hargitsi da rashin kwanciyar hankali a yankin.

“Duk irin wadannan shawarwari yunkuri ne na ingiza rikici,” a cewarsa, kamar yadda kamfanin dillanci labarai na Reuters ya rawaito.

Abu Zuhri ya kuma yi martani kan batun da Trump ke yi cewa a sake wa ‘yan Gaza matsugunai a kasashe da ke kurkusa, yana cewa wannan wani lamari ne na sake kunna wutar sabon rikici da tashin hankali a gabas ta tsakiya”.

“Mutanenmu da ke zirrin Gaza ba su yarda da wannan shiri ba. Abin da ake bukata shi ne kawo karshen mamaya da musgunawa mutane, ba raba su da yankinsu,” kamar yadda ya fadawa ‘yan jarida.

Kalaman Trump na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da kokari na shiga tsakani domin kawo karshen yakin Isra’ila da Hamas, a mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta da musayar fursunoni.

Kasashen Larabawa sun bijire

Saudiyya ta mayar da martani cikin gaggawa kan kudurin Trump na shirin kwace iko da zirin Gaza, inda ta yi watsi da duk wani yunkuri na raba Falasdinawa da kasarsu.

Saudiyyar ta ce ba za ta kulla wata alaka da Isra’ila ba har sai an samar da kasar Falasdinu.

Kasashen Masar da Jordan suma sun bayyana rashin amincewarsu da yunkurin na Trump na tsugunnar da Falasdinawa a kasashensu.

A wata sanarwar hadin-gwiwa, shugabannin kasashe daga Gabas Ta Tsakiya da kungiyoyi sun yi gargadi abin da ka iya biyo bayan wannan shiri, sannan sun ce babu wanda zai aminta da duk wani yunkuri na share wata al’umma ko rabata da asalinta.

Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya, Riyad Mansour, ya ce ‘yan Gaza na son komawa gidajensu da sake gina yankin, saboda nan ne “asalinsu kuma suna son rayuwa a inda yake nasu.”

“Ina ganin lokaci ya yi da ya kamata shugabanni su ke mutunta muradai da fatan Falasdinawa,” a cewarsa.

Gaza
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
Gaza
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
  • Sulaiman
    Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa
  • Sulaiman
    Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

MASU ALAKA

'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Xi Ya Umarci Ceto Daukacin Mutanen Da Suka Nutse A Ruftawar Kasar Da Ta Auku A Kudu Maso Yammacin Sin

Xi Ya Umarci Ceto Daukacin Mutanen Da Suka Nutse A Ruftawar Kasar Da Ta Auku A Kudu Maso Yammacin Sin

LABARAI MASU NASABA

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.