ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsanar Baki:’Yan Nijeriya Na Bukatar Daukin Gwamnatin Tarayya A Afirka Ta Kudu

by Yusuf Shuaibu
2 months ago
Tsanar

‘Yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta dauki matakan gaggawa wajen kare rayukansu da kasuwancinsu a kasar.

Shugaban kungiyar ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu (NICASA), Reb Frank Onyekwelu, shi ya yi wannan kira a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.

A halin yanzu akwai karuwar zanga-zangar adawa da bakin haure a fadin Afirka ta Kudu, inda masu zanga-zangar suka mayar da hankali kan shagunan da baki suka mallaka, yayin da suke kiran a kori wadanda ba ‘yan kasa ba.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa a ranar Juma’a, wacce mai magana da yawun hukumar kula da ‘yan Nijeriya da ke kasashen waje (NiDCOM), Abdur-Rahman Balogun, ya sanya hannu a kai, ta roki ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu da su rufe kasuwancinsu su kuma kasance cikin aminci.

Ya ce shawarar ta biyo ne bayan wata wasika daga ofishin jakadancin Nijeriya a Johannesburg a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

A cewar hukumar, zanga-zanga a Gabashin Landan, Cape Town, Durban, da KwaZulu-Natal sun rikide zuwa tashin hankali, wanda ya haifar da satar kayayyaki, lalata kadarori, da jakkata mutane.

NiDCOM ta ce bayanai daga ofishin jakadanci sun nuna cewa an shirya sabbin zanga-zanga a lardin Gauteng tsakanin ranakun 27 da 29 ga Afrilu, inda masu zanga-zangar ke neman matsa lamba ga gwamnatin Afirka ta Kudu ta kori ‘yan kasashen waje.

NiDCOM ta kuma yi kira ga ‘yan kasuwa na Nijeriya da su rufe shagunansu a ranar 27 ga Afrilu, wacce aka kebe a matsayin ranar ‘yanci, sannan su yi la’akari da ci gaba da rufe su a ranar 28 da 29 ga Afrilu, saboda galibi ana kai wa kasuwancin mallakar baki hari a yayin zanga-zangar.

Duk da haka, yawancin ‘yan Nijeriya sun shiga kafafen sada zumunta don su soki rashin matakin gwamnatin tarayya wajen kare ‘yan kasarta a Afirka ta Kudu, sun kara da cewa neman ‘yan Nijeriya su rufe kasuwancinsu ba shi ne mafita ga matsalar ba.

A daya bangaren, Ghana ta mayar da martani ga wani bidiyo da ya bazu na wasu ‘yan kasa da ke fuskantar tsangwama a Afirka ta Kudu ta hanyar kira ga mukaddashin babban kwamishanan Afirka ta Kudu da ke Accra, Thando Dalamba.

Ma’aikatar harkokin waje ta Ghana ta ce abin da ke cikin bidiyon wanda ya faru ga ‘yan kasarta a Afirka ta Kudu ta yi Allah-wadai da cin zarafin jama’arta.

Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Ablakwa, ya bayyana cewa gwamnati za ta mayar da wanda abin ya shafa, Emmanuel Asamoa, tare da ba shi kudade mai yawa bayan da ya fuskanci barazana da cin zarafi.

Gwamnatin Ghana ta kuma shiga tattaunawa kai tsaye da hukumomin Afirka ta Kudu, wanda ya kai ga bayar da hakuri na hukuma da tarurrukan diflomasiyya.

Tsanar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Next Post
2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.