ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsanar Baki:’Yan Nijeriya Na Bukatar Daukin Gwamnatin Tarayya A Afirka Ta Kudu

by Yusuf Shuaibu
1 month ago
Tsanar

‘Yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta dauki matakan gaggawa wajen kare rayukansu da kasuwancinsu a kasar.

Shugaban kungiyar ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu (NICASA), Reb Frank Onyekwelu, shi ya yi wannan kira a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.

A halin yanzu akwai karuwar zanga-zangar adawa da bakin haure a fadin Afirka ta Kudu, inda masu zanga-zangar suka mayar da hankali kan shagunan da baki suka mallaka, yayin da suke kiran a kori wadanda ba ‘yan kasa ba.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa a ranar Juma’a, wacce mai magana da yawun hukumar kula da ‘yan Nijeriya da ke kasashen waje (NiDCOM), Abdur-Rahman Balogun, ya sanya hannu a kai, ta roki ‘yan Nijeriya a Afirka ta Kudu da su rufe kasuwancinsu su kuma kasance cikin aminci.

Ya ce shawarar ta biyo ne bayan wata wasika daga ofishin jakadancin Nijeriya a Johannesburg a ranar Laraba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A cewar hukumar, zanga-zanga a Gabashin Landan, Cape Town, Durban, da KwaZulu-Natal sun rikide zuwa tashin hankali, wanda ya haifar da satar kayayyaki, lalata kadarori, da jakkata mutane.

NiDCOM ta ce bayanai daga ofishin jakadanci sun nuna cewa an shirya sabbin zanga-zanga a lardin Gauteng tsakanin ranakun 27 da 29 ga Afrilu, inda masu zanga-zangar ke neman matsa lamba ga gwamnatin Afirka ta Kudu ta kori ‘yan kasashen waje.

NiDCOM ta kuma yi kira ga ‘yan kasuwa na Nijeriya da su rufe shagunansu a ranar 27 ga Afrilu, wacce aka kebe a matsayin ranar ‘yanci, sannan su yi la’akari da ci gaba da rufe su a ranar 28 da 29 ga Afrilu, saboda galibi ana kai wa kasuwancin mallakar baki hari a yayin zanga-zangar.

Duk da haka, yawancin ‘yan Nijeriya sun shiga kafafen sada zumunta don su soki rashin matakin gwamnatin tarayya wajen kare ‘yan kasarta a Afirka ta Kudu, sun kara da cewa neman ‘yan Nijeriya su rufe kasuwancinsu ba shi ne mafita ga matsalar ba.

A daya bangaren, Ghana ta mayar da martani ga wani bidiyo da ya bazu na wasu ‘yan kasa da ke fuskantar tsangwama a Afirka ta Kudu ta hanyar kira ga mukaddashin babban kwamishanan Afirka ta Kudu da ke Accra, Thando Dalamba.

Ma’aikatar harkokin waje ta Ghana ta ce abin da ke cikin bidiyon wanda ya faru ga ‘yan kasarta a Afirka ta Kudu ta yi Allah-wadai da cin zarafin jama’arta.

Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Ablakwa, ya bayyana cewa gwamnati za ta mayar da wanda abin ya shafa, Emmanuel Asamoa, tare da ba shi kudade mai yawa bayan da ya fuskanci barazana da cin zarafi.

Gwamnatin Ghana ta kuma shiga tattaunawa kai tsaye da hukumomin Afirka ta Kudu, wanda ya kai ga bayar da hakuri na hukuma da tarurrukan diflomasiyya.

Tsanar
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.