Tsohon Sufeto Janar na ‘Yansanda, Mohammed Adamu Abubakar, ya bayyana cewa babu maganar amfani da tsarin masalaha (consensus) wajen zaɓen ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Nasarawa.
Tsohon shugaban ‘yansandan, wanda yake daga cikin manyan masu neman tikitin jam’iyyar, ya ce babu abin da za su amince da shi face zaɓen fidda gwani kai tsaye.
Ya bayyana hakan ne a Lafia ta bakin Daraktan Hulɗa da Wayar da Kai na kwamitin yaƙin neman zaɓensa, Hon. Isah Nathaniel, a ranar Asabar.
Nathaniel ya ce matsayar da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka cimma—ciki har da dukkan ‘yan takarar gwamna, ‘yan Majalisar Tarayya, tsofaffin gwamnoni biyu na jihar, da sauransu—a wani taro da aka yi a gidan gwamnatin jihar da ke Abuja, na nan daram.
Ya ƙara da cewa a wancan taro, an amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye a matsayin hanya kaɗai ta zaɓen ɗan takara, wanda ya yi daidai da ra’ayin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bai wa kowane ɗan jam’iyya damar bayyana ra’ayinsa.
Nathaniel ya bayyana cewa a wannan taro, Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya tabbatar cewa tsarin zai kasance a buɗe, mai gaskiya, kuma bisa dokokin jam’iyya da kundin dokar zaɓe, ta yadda ba za a samu ƙorafi ba.
Sai dai ya ce abin ya ba mutane da dama mamaki, ganin yadda bayan ‘yan kwanaki kaɗan aka fara maganar fifita wani ɗan takara.
A cewarsa, duk da cewa gwamnan na da ‘yancin goyon bayan duk wanda ya ga dama, hakan ba zai iya soke matsayar da masu ruwa da tsaki suka ɗauka ba, wadda ta amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye bisa dokokin jam’iyya da na zaɓe.
“Yanzu fara neman wata tattaunawa ko yarjejeniya a wannan lokaci tamkar ƙoƙarin kauce wa gaskiya ne.
“Mun ce a’a ga duk wani nau’in tilastawa ko son rai; muna tsayawa kan bin doka da oda,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa jagoransa ya riga ya sayi fom ɗin neman tsayawa takara da na nuna sha’awa kamar yadda doka ta tanada, yana mai cewa jama’a na jiran zaɓen fidda gwani ne kawai domin tabbatar da goyon bayansu gare shi.















Discussion about this post