ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

by Muhammad
1 month ago

Tsohon Sufeto Janar na ‘Yansanda, Mohammed Adamu Abubakar, ya bayyana cewa babu maganar amfani da tsarin masalaha (consensus) wajen zaɓen ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Nasarawa.

Tsohon shugaban ‘yansandan, wanda yake daga cikin manyan masu neman tikitin jam’iyyar, ya ce babu abin da za su amince da shi face zaɓen fidda gwani kai tsaye.

Ya bayyana hakan ne a Lafia ta bakin Daraktan Hulɗa da Wayar da Kai na kwamitin yaƙin neman zaɓensa, Hon. Isah Nathaniel, a ranar Asabar.

ADVERTISEMENT

Nathaniel ya ce matsayar da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka cimma—ciki har da dukkan ‘yan takarar gwamna, ‘yan Majalisar Tarayya, tsofaffin gwamnoni biyu na jihar, da sauransu—a wani taro da aka yi a gidan gwamnatin jihar da ke Abuja, na nan daram.

Ya ƙara da cewa a wancan taro, an amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye a matsayin hanya kaɗai ta zaɓen ɗan takara, wanda ya yi daidai da ra’ayin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bai wa kowane ɗan jam’iyya damar bayyana ra’ayinsa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Nathaniel ya bayyana cewa a wannan taro, Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya tabbatar cewa tsarin zai kasance a buɗe, mai gaskiya, kuma bisa dokokin jam’iyya da kundin dokar zaɓe, ta yadda ba za a samu ƙorafi ba.

Sai dai ya ce abin ya ba mutane da dama mamaki, ganin yadda bayan ‘yan kwanaki kaɗan aka fara maganar fifita wani ɗan takara.

A cewarsa, duk da cewa gwamnan na da ‘yancin goyon bayan duk wanda ya ga dama, hakan ba zai iya soke matsayar da masu ruwa da tsaki suka ɗauka ba, wadda ta amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye bisa dokokin jam’iyya da na zaɓe.

“Yanzu fara neman wata tattaunawa ko yarjejeniya a wannan lokaci tamkar ƙoƙarin kauce wa gaskiya ne.

“Mun ce a’a ga duk wani nau’in tilastawa ko son rai; muna tsayawa kan bin doka da oda,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jagoransa ya riga ya sayi fom ɗin neman tsayawa takara da na nuna sha’awa kamar yadda doka ta tanada, yana mai cewa jama’a na jiran zaɓen fidda gwani ne kawai domin tabbatar da goyon bayansu gare shi.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Wadanne Kasashe Ne Ba Su Taba Zuwa Kofin Afirka Ba?

FIFA Ta Kara Yawan Kudaden Da Za Ta Bai Wa Kasashen Da Suke Buga Gasar Kofin Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.