ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Babu Maganar Masalaha A APC Ta Nasarawa — Tsohon Sufeto Janar Na ‘Yansanda

by Muhammad
2 months ago

Tsohon Sufeto Janar na ‘Yansanda, Mohammed Adamu Abubakar, ya bayyana cewa babu maganar amfani da tsarin masalaha (consensus) wajen zaɓen ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a Jihar Nasarawa.

Tsohon shugaban ‘yansandan, wanda yake daga cikin manyan masu neman tikitin jam’iyyar, ya ce babu abin da za su amince da shi face zaɓen fidda gwani kai tsaye.

Ya bayyana hakan ne a Lafia ta bakin Daraktan Hulɗa da Wayar da Kai na kwamitin yaƙin neman zaɓensa, Hon. Isah Nathaniel, a ranar Asabar.

ADVERTISEMENT

Nathaniel ya ce matsayar da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka cimma—ciki har da dukkan ‘yan takarar gwamna, ‘yan Majalisar Tarayya, tsofaffin gwamnoni biyu na jihar, da sauransu—a wani taro da aka yi a gidan gwamnatin jihar da ke Abuja, na nan daram.

Ya ƙara da cewa a wancan taro, an amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye a matsayin hanya kaɗai ta zaɓen ɗan takara, wanda ya yi daidai da ra’ayin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na bai wa kowane ɗan jam’iyya damar bayyana ra’ayinsa.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

Nathaniel ya bayyana cewa a wannan taro, Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya tabbatar cewa tsarin zai kasance a buɗe, mai gaskiya, kuma bisa dokokin jam’iyya da kundin dokar zaɓe, ta yadda ba za a samu ƙorafi ba.

Sai dai ya ce abin ya ba mutane da dama mamaki, ganin yadda bayan ‘yan kwanaki kaɗan aka fara maganar fifita wani ɗan takara.

A cewarsa, duk da cewa gwamnan na da ‘yancin goyon bayan duk wanda ya ga dama, hakan ba zai iya soke matsayar da masu ruwa da tsaki suka ɗauka ba, wadda ta amince da zaɓen fidda gwani kai tsaye bisa dokokin jam’iyya da na zaɓe.

“Yanzu fara neman wata tattaunawa ko yarjejeniya a wannan lokaci tamkar ƙoƙarin kauce wa gaskiya ne.

“Mun ce a’a ga duk wani nau’in tilastawa ko son rai; muna tsayawa kan bin doka da oda,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jagoransa ya riga ya sayi fom ɗin neman tsayawa takara da na nuna sha’awa kamar yadda doka ta tanada, yana mai cewa jama’a na jiran zaɓen fidda gwani ne kawai domin tabbatar da goyon bayansu gare shi.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
Wadanne Kasashe Ne Ba Su Taba Zuwa Kofin Afirka Ba?

FIFA Ta Kara Yawan Kudaden Da Za Ta Bai Wa Kasashen Da Suke Buga Gasar Kofin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.