A wata Sanarwa Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu na jihar Ahmed Maiyaki ya fitar, ta bayyana cewa kudin ya shafi tsarin asusun fansho da kudin barin aiki dana mutuwa a wani bangare na kokarin gwamnati na rage basussukan fensho da inganta tsarin walwalar jama’a.
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya amince da sakin kudi Naira biliyan 4.289 domin biyan hakkokin ‘yan fensho, kudaden ritaya da kuma tallafin mutuwa ga tsofaffin ma’aikata da iyalan wadanda suka rasu a matakan Jiha da Kananan Hukumomi.
Ahmed Maiyaki, yace wannan mataki na nuna irin salon shugabancin da ke mayar da hankali kan jin dadin jama’a da kuma tabbatar da mutunci ga tsofaffin ma’aikata.“Wannan ba wai kawai biyan bashi ba ne, yana nufin dawo da mutunci da karrama hidimar da ma’aikata suka yi wa kasa tsawon shekaru,” in ji shi.
Ya kara da cewa, tun bayan hawan mulkin Uba Sani, gwamnatin ta riga ta kashe jimillar Naira biliyan 17.796 wajen biyan fensho, inda sama da mutane 8,344 suka amfana, ciki har da iyalan wadanda suka rasu.Kwamishinan ya jaddada cewa wannan mataki wani bangare ne na manyan gyare-gyaren da gwamnati ke yi domin tabbatar da gaskiya, inganta kula da kudaden gwamnati, da kuma dorewar tsarin biyan fensho.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace domin tabbatar da ana biyan hakkokin fensho a kan lokaci, tare da kare mutuncin ma’aikata bayan sun yi ritaya.
Gwamnatin jihar, a cewarsa, na da kudurin tabbatar da cewa ma’aikata suna ritaya cikin kwanciyar hankali, girmamawa, da jin cikar burinsu bayan sun sadaukar da rayuwarsu wajen hidimar jama’a.















Discussion about this post