Shugaban Majalisar Kawar da Zazzabin Cizon Sauro ta Ƙasa (NMEC) kuma jakadan Majalisar Ɗinkin Duniya kan cutar, Aliko Dangote, ya buƙaci gwamnatoci da kamfanoni masu zaman kansu su ƙara ƙaimi wajen ɗaukar matakan haɗin gwuiwa domin kawo ƙarshen cutar, yana mai cewa lokaci ya yi da ya dace a ɗauki mataki mai ƙarfi. Ya bayyana haka ne yayin bikin Ranar Zazzabin Cizon Sauro ta Duniya ta 2026.
Dangote ya ce duk da an samu ci gaba a yaƙi da cutar, har yanzu ba a daidaita wannan ci gaban ba, musamman a yankin Afirka ta kudu da Sahara da ke ɗauke da sama da kashi 90 cikin 100 na masu fama da cutar a duniya. Ya ƙara da cewa cutar na ci gaba da shafar yara ƙanana, da mata masu juna biyu da kuma al’umma marasa galihu, tare da jefa tsarin kiwon lafiya da tattalin arziƙi cikin matsin lamba.
Ya jaddada cewa duk da cigaban kimiyya kamar sabbin alluran rigakafi, da ingantattun hanyoyin gano cuta da kuma tsarin sa ido na zamani, akwai buƙatar aiwatar da waɗannan hanyoyi cikin gaggawa da adalci. A cewarsa, hanyar kawar da cutar ta fi bayyana yanzu fiye da kowane lokaci, amma abin da ake buƙata shi ne aiwatarwa mai faɗi da haɗin kai.
Haka kuma, Dangote ya yi kira da a ƙarfafa haɗin gwuiwa tsakanin gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu, yana mai gargaɗin cewa ƙalubale kamar juriyar magunguna da sinadarai na iya kawo cikas. Ya ce wajibi ne a ci gaba da zuba jari da haɗa kai domin tabbatar da cewa an kawar da cutar gaba ɗaya.















Discussion about this post