• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya

by Rabi'u Ali Indabawa and Usman Abubakar
2 years ago
in Manyan Labarai
0
…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ya rage kwanaki kalilan a rantsar da Bola Ahmed Tinubu a matsayin sabon shugaban Nijeriya, wasu mashahuran ‘yan jarida da ke farauto labarai a fadar shugaban kasa, sun yi waiwaye adon tafiya a kan yadda ake tafiyar da harkokin mika mulki.

Har ila yau, domin fayyace abubuwan da suke faruwa a wajen bikin mika mulkin, ciki har da halartar manyan baki da kuma jawabai na tunawa da sabon shugaban da aka rantsar, ’yan jaridar, wadanda aka fi sani da wakilan gidan gwamnati, sun yi wa LEADERSHIP Hausa karin bayani kan abubuwan da za su kayatar a wajen bikin rantsuwar.
Wani babban da jarida mai suna Chesa Chesa, wadda ke daukar rahoto a fadar gwamnati tun a shekarar 2008, ya ce dama an saba, duk lokacin da za a mika mulki ga sabuwar gwamnati akan shirya gudanar da abubuwa da dama.

  • Ranar Afirka Ita Ma Rana Ce Ta Kasar Sin

A cewarsa, an mai da hankali sosai kan jawabin shugaban kasa mai jiran gado, inda da yawa ke jiran su ji sanarwa ko yanke shawara da za su nuna alkiblar sabuwar gwamnati.

Ya ce jama’a, wadanda aka gayyata da wadanda ba a gayyace su ba, sun yi cincirindo a dandalin Eagle Skuare, wanda ‘yan sanda suka yi wa tsinke. Yanayin yawanci kamar biki ne. Har ma a wajen dandalin Eagle Skuare inda ake rera wakoki ga sunan sabon shugaban kasa da jam’iyyarsa ta hayar kida.

“Ana kewaye filin rantsar da shugaban kasa da jami’an tsaro. Sannan mutane kan yi kasuwanci daga nesa da harabar filin.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

“Akan mai da hankali sosai kan shugaban kasa, kuma ba a kan mataimakin shugaban kasa ba. A ko da yaushe akwai shugabannin da ke kawo ziyara, musamman shugabannin Afirka. Yana daya daga cikin lokutan da sojoji da jami’an tsaro ke yin, fareti.

“Yawanci a kan yi raye-raye masu ban sha’awa da wasan kwaikwayo, wadanda ke nuna manyan kabilun kasa. Tabbas, baki, musamman masu manya-manya kan halarci taron cikin shiga ta alfarma.
“Abin sha’awa shi ne, za a ga shugaba mai barin gado tare da rakiyar matarsa. Bayan rantsar da sabon shugaban da mataimakinsa, shugaban da mataimakinsa mai barin gado sukan bar sashen manyan baki. Dukka bikin yana daukar kimanin sa’o’i uku ne ko fiye da haka,” in ji Chesa.

Wani babban da jarida, Sunday Ode, wanda bai wuce shekaru 13 ba a matsayin wakilin gidan gwamnati ya tafka muhawara a kan kudirin shugaban kasa, ya tuno jawabin shugaban kasa Muhammadu Buhari mai barin gado, inda ya ce shi na kowa ne, sannan ba kowa ba.

Ode wanda ya yi tsokaci kan bikin rantsar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo karo na biyu, da kuma bikin rantsar da Marigayi Umaru Musa ‘Yar’adua, Goodluck Jonathan da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, “Kamar ‘yan siyasa, yawanci yana daya daga cikin abubuwan da ‘yan jarida ke sa rai tare da kyakkyawan fata dangane da batun fayyace bayanai da kuma alkawuran da kowane sabon shugaban kasa zai yi.
“Kar ku manta Yar’Adua ya girgiza duniya lokacin da ya bayyana cewa zaben da ya haifar da shi bai inganta ba. Kuma kar ku manta Buhari ya ce “Ni na kowa ne, ba na kowa ba ne”.

“Faretin sojoji yawanci abin kallo ne a duk taron kaddamar da ko dai wadanda ke kasa a dandalin Eagle Skuare ko kuma wadanda ke kallo daga nesa”.
Ode ya ci gaba da cewa, babban lokacin da ake gudanar da duk wani nadin sarauta, musamman ma wanda ya kawo sabuwar gwamnati, shi ne lokacin da shugaban kasa mai barin gado ya sauka daga mukaminsa kamar yadda aka yi tsakanin Jonathan da Buhari.

A halin da ake ciki kuma, babban mai fafutukar kare hakkin bil’adama, kuma kwararre a fannin shari’a, Cif Olisa Agbakoba (SAN), a jiya ya ce rashin tabbas da aka samu a bikin rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, zai sa taron ya zama abin tunawa.

Agbakoba, babban jigo a fafutukar tabbatar da dimokuradiyyar kasa, ya jaddada cewa kararrakin da ake jira ba zai iya dakatar da kaddamar da shirin mika mulki ba, inda ya kara da cewa ba zai iya tunawa akwai wani lokaci da aka gabatar da irin wadannan koke-koke na dakatar da bikin rantsuwa ba.

Ya ce, “Batun da ya fi muhimmanci kamar yadda nake gani, shi ne damuwar ko za a yi bikin rantsuwa. Ina ganin wannan shi ne batun da ya fi daukar hankali wanda zai sa bikin ya zama abin ban mamaki fiye da sauran.
“A gare ni da kaina, ta fuskar doka, wannan bikin ba za a iya hana shi gudana ba saboda abin da ya faru, cewa an shigar da kara a kotu don haka dole ne mu jira.

“Abin mamaki game da ni a ce an hana yin rantsuwa. Wannan shi ne abin mamaki a gare ni.
Shi ma da yake nasa jawabin, Sanata Femi Okurounmu ya ce bai kamata a ce rantsar da zababbun masu mukamai ya samu tasgaro ba.
Sai dai ya ce abin da ake sa rai daga shugaban kasa mai jiran gado shi ne zai magance matsalolin da ke addabar Nijeriya.

Ya ce, “Ba matsalolin da ‘yan Nijeriya ke son a magance su kadai ba, a’a, wasu matsalolin da shi da kansa ya yi a lokacin da yake karkashin Cif Obafemi Awolowo da Abraham Adesanya ya kwashe tsawon wadannan shekaru kafin ya koma APC. Ina fata har yanzu zai tuna da wadannan abubuwan kuma ya kula da su.
‘’Sauran abin da ake sa rai shi ne ya koma tsarin mulkin 1953. Wannan yana daya daga cikin fifikon farko. Kundin tsarin mulkin da muke aiki da shi a yanzu yaudara ne, almubazzaranci ne, yana da tsada, mulkin kama karya ne, ba dimokradiyya ba.

“Idan ya koma ga kundin tsarin mulki na 1953, tare da gyare-gyaren da ya kamata, abin da nake ji shi ne, mu koma ga Jihohi 12 na Janar Yakubu Gowon (mai ritaya) da aka kirkira lokacin yana shugaban kasa na soja.”
A kan yadda hakan zai iya kasancewa, Okurounmu ya ce, ”Na ce ya koma wancan tsarin. Idan ya yarda ya koma tsarin, me ya sa hakan bai tabbata ba? Mun gudanar da jihohi 12 a karkashin Gowon; za mu iya komawa tsarin. Kuma mun gudanar da kundin tsarin mulki na 1953- shi ne abin da muka yi aiki daga 1960 zuwa 1966 kuma ya yi mana amfani sosai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ruguntsumin Rantsar Da Sabuwar Gwamnati: Abubuwa 10 Da Suka Kamata A Sani

Next Post

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

3 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

5 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

6 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

16 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

17 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

23 hours ago
Next Post
Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.