• Leadership Hausa
Monday, May 29, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya

by Rabi'u Ali Indabawa and Usman Abubakar
3 days ago
in Manyan Labarai
0
…Waiwaye Game Da Yadda Aka Rantsar Da Wasu Shugabanni Na Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da ya rage kwanaki kalilan a rantsar da Bola Ahmed Tinubu a matsayin sabon shugaban Nijeriya, wasu mashahuran ‘yan jarida da ke farauto labarai a fadar shugaban kasa, sun yi waiwaye adon tafiya a kan yadda ake tafiyar da harkokin mika mulki.

Har ila yau, domin fayyace abubuwan da suke faruwa a wajen bikin mika mulkin, ciki har da halartar manyan baki da kuma jawabai na tunawa da sabon shugaban da aka rantsar, ’yan jaridar, wadanda aka fi sani da wakilan gidan gwamnati, sun yi wa LEADERSHIP Hausa karin bayani kan abubuwan da za su kayatar a wajen bikin rantsuwar.
Wani babban da jarida mai suna Chesa Chesa, wadda ke daukar rahoto a fadar gwamnati tun a shekarar 2008, ya ce dama an saba, duk lokacin da za a mika mulki ga sabuwar gwamnati akan shirya gudanar da abubuwa da dama.

  • Ranar Afirka Ita Ma Rana Ce Ta Kasar Sin

A cewarsa, an mai da hankali sosai kan jawabin shugaban kasa mai jiran gado, inda da yawa ke jiran su ji sanarwa ko yanke shawara da za su nuna alkiblar sabuwar gwamnati.

Ya ce jama’a, wadanda aka gayyata da wadanda ba a gayyace su ba, sun yi cincirindo a dandalin Eagle Skuare, wanda ‘yan sanda suka yi wa tsinke. Yanayin yawanci kamar biki ne. Har ma a wajen dandalin Eagle Skuare inda ake rera wakoki ga sunan sabon shugaban kasa da jam’iyyarsa ta hayar kida.

“Ana kewaye filin rantsar da shugaban kasa da jami’an tsaro. Sannan mutane kan yi kasuwanci daga nesa da harabar filin.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya

Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu

“Akan mai da hankali sosai kan shugaban kasa, kuma ba a kan mataimakin shugaban kasa ba. A ko da yaushe akwai shugabannin da ke kawo ziyara, musamman shugabannin Afirka. Yana daya daga cikin lokutan da sojoji da jami’an tsaro ke yin, fareti.

“Yawanci a kan yi raye-raye masu ban sha’awa da wasan kwaikwayo, wadanda ke nuna manyan kabilun kasa. Tabbas, baki, musamman masu manya-manya kan halarci taron cikin shiga ta alfarma.
“Abin sha’awa shi ne, za a ga shugaba mai barin gado tare da rakiyar matarsa. Bayan rantsar da sabon shugaban da mataimakinsa, shugaban da mataimakinsa mai barin gado sukan bar sashen manyan baki. Dukka bikin yana daukar kimanin sa’o’i uku ne ko fiye da haka,” in ji Chesa.

Wani babban da jarida, Sunday Ode, wanda bai wuce shekaru 13 ba a matsayin wakilin gidan gwamnati ya tafka muhawara a kan kudirin shugaban kasa, ya tuno jawabin shugaban kasa Muhammadu Buhari mai barin gado, inda ya ce shi na kowa ne, sannan ba kowa ba.

Ode wanda ya yi tsokaci kan bikin rantsar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo karo na biyu, da kuma bikin rantsar da Marigayi Umaru Musa ‘Yar’adua, Goodluck Jonathan da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce, “Kamar ‘yan siyasa, yawanci yana daya daga cikin abubuwan da ‘yan jarida ke sa rai tare da kyakkyawan fata dangane da batun fayyace bayanai da kuma alkawuran da kowane sabon shugaban kasa zai yi.
“Kar ku manta Yar’Adua ya girgiza duniya lokacin da ya bayyana cewa zaben da ya haifar da shi bai inganta ba. Kuma kar ku manta Buhari ya ce “Ni na kowa ne, ba na kowa ba ne”.

“Faretin sojoji yawanci abin kallo ne a duk taron kaddamar da ko dai wadanda ke kasa a dandalin Eagle Skuare ko kuma wadanda ke kallo daga nesa”.
Ode ya ci gaba da cewa, babban lokacin da ake gudanar da duk wani nadin sarauta, musamman ma wanda ya kawo sabuwar gwamnati, shi ne lokacin da shugaban kasa mai barin gado ya sauka daga mukaminsa kamar yadda aka yi tsakanin Jonathan da Buhari.

A halin da ake ciki kuma, babban mai fafutukar kare hakkin bil’adama, kuma kwararre a fannin shari’a, Cif Olisa Agbakoba (SAN), a jiya ya ce rashin tabbas da aka samu a bikin rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, zai sa taron ya zama abin tunawa.

Agbakoba, babban jigo a fafutukar tabbatar da dimokuradiyyar kasa, ya jaddada cewa kararrakin da ake jira ba zai iya dakatar da kaddamar da shirin mika mulki ba, inda ya kara da cewa ba zai iya tunawa akwai wani lokaci da aka gabatar da irin wadannan koke-koke na dakatar da bikin rantsuwa ba.

Ya ce, “Batun da ya fi muhimmanci kamar yadda nake gani, shi ne damuwar ko za a yi bikin rantsuwa. Ina ganin wannan shi ne batun da ya fi daukar hankali wanda zai sa bikin ya zama abin ban mamaki fiye da sauran.
“A gare ni da kaina, ta fuskar doka, wannan bikin ba za a iya hana shi gudana ba saboda abin da ya faru, cewa an shigar da kara a kotu don haka dole ne mu jira.

“Abin mamaki game da ni a ce an hana yin rantsuwa. Wannan shi ne abin mamaki a gare ni.
Shi ma da yake nasa jawabin, Sanata Femi Okurounmu ya ce bai kamata a ce rantsar da zababbun masu mukamai ya samu tasgaro ba.
Sai dai ya ce abin da ake sa rai daga shugaban kasa mai jiran gado shi ne zai magance matsalolin da ke addabar Nijeriya.

Ya ce, “Ba matsalolin da ‘yan Nijeriya ke son a magance su kadai ba, a’a, wasu matsalolin da shi da kansa ya yi a lokacin da yake karkashin Cif Obafemi Awolowo da Abraham Adesanya ya kwashe tsawon wadannan shekaru kafin ya koma APC. Ina fata har yanzu zai tuna da wadannan abubuwan kuma ya kula da su.
‘’Sauran abin da ake sa rai shi ne ya koma tsarin mulkin 1953. Wannan yana daya daga cikin fifikon farko. Kundin tsarin mulkin da muke aiki da shi a yanzu yaudara ne, almubazzaranci ne, yana da tsada, mulkin kama karya ne, ba dimokradiyya ba.

“Idan ya koma ga kundin tsarin mulki na 1953, tare da gyare-gyaren da ya kamata, abin da nake ji shi ne, mu koma ga Jihohi 12 na Janar Yakubu Gowon (mai ritaya) da aka kirkira lokacin yana shugaban kasa na soja.”
A kan yadda hakan zai iya kasancewa, Okurounmu ya ce, ”Na ce ya koma wancan tsarin. Idan ya yarda ya koma tsarin, me ya sa hakan bai tabbata ba? Mun gudanar da jihohi 12 a karkashin Gowon; za mu iya komawa tsarin. Kuma mun gudanar da kundin tsarin mulki na 1953- shi ne abin da muka yi aiki daga 1960 zuwa 1966 kuma ya yi mana amfani sosai.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ruguntsumin Rantsar Da Sabuwar Gwamnati: Abubuwa 10 Da Suka Kamata A Sani

Next Post

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Related

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya

1 day ago
Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu
Manyan Labarai

Ganduje Zai Mika Wa Abba Gida-Gida Ragamar Mulkin Kano, Don Halartar Rantsar Da Tunibu

1 day ago
Na Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Na Same Ta A 2015 – Buhari
Manyan Labarai

Na Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Na Same Ta A 2015 – Buhari

1 day ago
An Ci Gaba Da Jefa Kuri’a A Zaben Turkiyya Zagaye Na Biyu A Yau Lahadi
Manyan Labarai

An Ci Gaba Da Jefa Kuri’a A Zaben Turkiyya Zagaye Na Biyu A Yau Lahadi

1 day ago
Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima
Manyan Labarai

Ba Ma Kokarin Musuluntar Da Nijeriya –Shettima

2 days ago
Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sauya Jam’iyya Ba -NNPP

2 days ago
Next Post
Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

Mika Mulki: Yadda Buhari Ya Fara Damka Ragamar Shugabancin Nijeriya A Hannun Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

An Rantsar Da Gwamna Bala Muhammad A Matsayin Gwamnan Bauchi A Karo Na 2

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Jagoranci Za Mu Yi Ba Mulkin ‘Yan Nijeriya Ba – Tinubu

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

Da Dumi-dumi: Justis Hafsat Ta Rantsar Da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri

May 29, 2023
Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

Da Dumi-dumi: An Rantsar Da Tinubu A Matsayin Shugaban Nijeriya Na 16

May 29, 2023
A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

A Dan Lokacin Da Ya Rage Kafin Mika Mulki: Buhari Ya Sauya Sunayen Filayen Jiragen Sama 15

May 29, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

May 29, 2023
Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

Bankwana Da Gwamnatin Buhari: Hukumar Tsaron Cikin Gida Ta Kara Wa Jami’ai 17,331 Matsayi

May 29, 2023
Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

Gwamnati Ta Samar Da Tan 89,512 Na Irin Noma A Bana – Minista

May 29, 2023
Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

Kwana Guda Ya Sauka, El-Rufai Ya Haramta Kungiyar Kudancin Kaduna

May 29, 2023
Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

Buhari Ya Nada Sha’aban Mukamin Babban Sakataren Hukumar Kula Da Almajirai Ta Nijeriya

May 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.