Ministan harkokin wajen Sin Wang Yi, ya ce Sin da Turai abokan hulda ne ba na gaba ba, kuma ya kamata hadin gwiwa a tsakaninsu ya zama tubali kuma muhimmiyar siga ta dangantakar Sin da Turai.
Wang Yi wanda mamba ne na ofishin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ya nanata matsayar ta kasar Sin ne a jiya Alhamis, yayin ganawarsa da takwaransa na Denmark Lars Lokke Rasmussen a Copenhagen.
Kasar Denmark ce zangonsa na farko cikin ziyarar mako 1 da zai yi a kasashe 4 na arewacin Turai da suka hada da Denmark da Sweden da Finland da Norway. (Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/














