ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Zargi Wasu ‘Yan Siyasar Ribas Da Ziga Fubara, Ya Ce Dole A Girmama Yarjejeniya

by Sadiq Usman
8 months ago
Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya zargi wasu jagororin siyasa a Jihar Ribas da ziga Gwamna Siminalayi Fubara.

Da yake jawabi ga magoya bayansa a Ƙaramar Hukumar Ogu/Bolo, Wike ya ce dole ne a girmama yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a gaban Shugaba Bola Tinubu domin kawo ƙarshen rikicin siyasa a jihar.

  • Sakataren APC Ya Buƙaci Murabus Ɗin Wike Saboda “Tsoma Baki” A Harkokin Jam’iyya
  • AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

Ya ce Gwamna Fubara bai bi ƙa’idojin yarjejeniyar ba, duk da cewa manyan shugabanni sun sanya hannu a kanta, ciki har da tsohon gwamna Peter Odili, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu, da sauran shugabannin jam’iyyu.

ADVERTISEMENT

Wike ya soki ‘yan siyasar da suka amince da yarjejeniyar amma daga baya suka fara faɗar akasin haka, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya jaddada cewa Jihar Ribas na da muhimmanci a siyasar yankin Kudu maso Kudu, kuma ya buƙaci shugabanni su riƙa faɗin gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Ya kuma tuno da yunƙurin da wasu ɓangarori suka yi a baya na rusa tsarin jam’iyyar PDP a jihar.

Wike ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa naɗa ‘yan asalin Ribas a manyan muƙaman tarayya, yana cewa Shugaban ya cika alƙawuran da ya ɗauka.

Wasu masu jawabi a taron, ciki har da shugaban Ribas Ijaw Peoples Congress, George Sekibo, sun nuna goyon bayansu ga Wike tare da sukar Gwamna Fubara.

Shugabannin yankin Ogu/Bolo ma sun yaba wa Wike bisa ayyukan ci gaba da naɗe-naɗen muƙamai da ya samar musu.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa, sarakunan gargajiya da sauran al’ummar yankin.

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Guterres Ya Zargi Amurka Da Take Dokar Ƙasa Da Ƙasa A Venezuela

Guterres Ya Zargi Amurka Da Take Dokar Ƙasa Da Ƙasa A Venezuela

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Wike

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Wike

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.