ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Zargi Wasu ‘Yan Siyasar Ribas Da Ziga Fubara, Ya Ce Dole A Girmama Yarjejeniya

by Sadiq Usman
5 months ago
Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya zargi wasu jagororin siyasa a Jihar Ribas da ziga Gwamna Siminalayi Fubara.

Da yake jawabi ga magoya bayansa a Ƙaramar Hukumar Ogu/Bolo, Wike ya ce dole ne a girmama yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a gaban Shugaba Bola Tinubu domin kawo ƙarshen rikicin siyasa a jihar.

  • Sakataren APC Ya Buƙaci Murabus Ɗin Wike Saboda “Tsoma Baki” A Harkokin Jam’iyya
  • AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

Ya ce Gwamna Fubara bai bi ƙa’idojin yarjejeniyar ba, duk da cewa manyan shugabanni sun sanya hannu a kanta, ciki har da tsohon gwamna Peter Odili, Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu, da sauran shugabannin jam’iyyu.

ADVERTISEMENT

Wike ya soki ‘yan siyasar da suka amince da yarjejeniyar amma daga baya suka fara faɗar akasin haka, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya jaddada cewa Jihar Ribas na da muhimmanci a siyasar yankin Kudu maso Kudu, kuma ya buƙaci shugabanni su riƙa faɗin gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya kuma tuno da yunƙurin da wasu ɓangarori suka yi a baya na rusa tsarin jam’iyyar PDP a jihar.

Wike ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa naɗa ‘yan asalin Ribas a manyan muƙaman tarayya, yana cewa Shugaban ya cika alƙawuran da ya ɗauka.

Wasu masu jawabi a taron, ciki har da shugaban Ribas Ijaw Peoples Congress, George Sekibo, sun nuna goyon bayansu ga Wike tare da sukar Gwamna Fubara.

Shugabannin yankin Ogu/Bolo ma sun yaba wa Wike bisa ayyukan ci gaba da naɗe-naɗen muƙamai da ya samar musu.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa, sarakunan gargajiya da sauran al’ummar yankin.

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Guterres Ya Zargi Amurka Da Take Dokar Ƙasa Da Ƙasa A Venezuela

Guterres Ya Zargi Amurka Da Take Dokar Ƙasa Da Ƙasa A Venezuela

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.