Gwamnatin Jihar Kwara ta shigar da ƙara a Babbar Kotun Jihar da ke Ilorin a kan tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, bisa zargin ɓata sunan Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ta hanyar wallafa kalaman da gwamnatin ta ce ƙarya ne.
A cewar takardar ƙarar, an zargi Saraki da yaɗa wani bayani a kafafen sada zumunta da kuma jaridu a ranar 17 ga Afrilu, 2026, inda aka yi iƙirarin cewa Gwamna AbdulRazaq bai mallaki takardar karatun sakandare ba. Gwamnatin jihar ta ce zargin ƙarya ne kuma an yi shi ne da nufin cin mutuncin gwamnan da tayar da hankalin jama’a.
A zaman kotun da aka yi ranar Laraba, lauyan gwamnati ya buƙaci kotu ta bayar da sammacin kama Saraki saboda rashin halartarsa domin gurfanar da shi, yana mai cewa an riga an miƙa masa takardun karar.
Sai dai lauyan Saraki, Jimoh Mumini (SAN), ya ƙalubalanci ikon Babbar Kotun Jihar Kwara na sauraron ƙarar, yana mai cewa wannan lamari ya kamata ya kasance a gaban Babbar Kotun Tarayya. Haka kuma ya yi tambaya kan yadda aka miƙa wa wanda yake karewa takardun ƙarar.
Bayan sauraron ɓangarorin biyu, Mai Shari’a M.O. Folorunso ya amince da buƙatar ɗage shari’ar, inda ya sanya ranar 3 ga Yuli, 2026 domin sauraron ƙorafin da aka yi kan ikon kotun da kuma yiwuwar gurfanar da Saraki.















Discussion about this post