Sakatare janar na kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya bukaci a yi kokarin karfafa jagorancin siyasa da zurfafa ci gaba ta hanyar kirkire-kirkire domin bunkasa zamantar da tsarin tsaron kasar da rundunoninta na soji.
Xi Jinping ya bayyana haka ne lokacin da yake jagorantar zaman nazari na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS a jiya Alhamis.
Shugaba Xi ya kuma bukaci a kokarin cimma dukkan burikan cikar rundunar ’yantar da al’ummar kasar Sin (PLA) shekaru 100 da kafuwa a shekarar 2027 da samun ingantaccen ci gaba wajen cimma zamanantar da tsarin tsaron kasar da rundunoninta na soji. A cewarsa, wannan zai samar da dabara mai karfi da za ta tallafa wa inganta gina babbar kasa da cimma farfadowar kasar ta kowacce fuska ta hanyar zamanantar da kanta.
An gudanar da taron nazari ne gabanin bikin kafuwar rundunar PLA a ranar 1 ga watan Augusta. A madadin kwamitin kolin JKS da hukumar koli mai kula da ayyukan soji, shugaba Xi ya mika gaisuwar ranar ga dukkan mambobin rundunar da rundunar ’yan sandan Sin da jami’ai fararen hula da ke aiki a rundunar PLA da sojojin da ake kira a lokacin bukata da kuma ’yan sa kai. (Fa’iza Mustapha)














