ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

by Rabi'at Sidi Bala
3 weeks ago

Kamar kowane mako, a yau ma shafin na tafe da wata baƙuwar ta musamman, inda shafin yayi cozali da wata fitacciyar mawaƙiya wacce ake yi wa laƙabi da Gimbiyar Sha’iran Ƙasar Hausa, kana Jakadiyar Galadiman Kano wato,  FATIMA ILIYASU ABUBAKAR wacce aka fi sani da FATI UK. Inda ta bayyanawa masu karatu batutuwa da suka shafi sana’ar waƙar ta, tare da batutuwan da suka shafi rayuwarta.

Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar jaridar LEADERSHIP HAUSA RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanki

ADVERTISEMENT

Sunana Fatima Iliyasu Abubakar, amma ana kira na da Fati UK

Ko za ki iya faɗawa masu karatu ɗan taƙaitaccen tarihinki?

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

An haifeni a Kano, ƙaramar hukumar Tarauni, a wata unguwa da ake kira da Darmanawa, bayan asibitin Aminu Kano. Na yi ‘Primary School’ a Kano, na yi ‘secondary school’ a Kano. A lokacin da nake ‘Secondary school’ ne na samu wannan sunan na Fati UK.

Me ya ja hankalinki har ki ka fara waƙa?

To, Alhamdulillah duk wanda zai ce ya fara harkar waƙa ko waƙe, abin da yake jan hankalinshi na farko dai yana ji kamar yana da baiwar ta wannan abun. Na biyu kuma ƙaddarar shi tana cika abun, na uku kuma yana so ya yi.

Kamar wacce irin waƙa ki ke yi?

A lokacin da na fara waƙa, ni na fara waƙoƙi na yabon Annabi (S.a.w) ne. Asali ni rubuta ƙasida nake, daga baya kuma yanayi na idan za ka yabi Annabi (S.a.w), ba komai za ka kira shi da shi ba, sai na riƙa na jure, saboda idan zan yi yabo sai na kai wa malamai sun tantance min, daga ƙarshe kuma sai na koma mawaƙiya ta siyasa.

Za ki yi kamar shekara nawa kina waƙa?

A taƙaice dai zan iya samun kamar shekara 20 ina yi waƙa.

Ya gwagwarmayar farawar ta kasance a wancen lokacin?

Gaskiya inda na fara gwagwarmaya lokacin dana fara waƙoƙi kamar na siyasa, tunda daman na faɗa miki ‘da’ waƙoƙin yabo nake yi na Manzon Allah (S.a.w), dana koma waƙoƙin siyasa gaskiya ita tana cike da gwagwarmaya da ƙalubale. Shi kuwa waƙoƙin yabo, saboda Annabi (S.a.w) za a yi wa, ba a buƙatar komai, ana buƙatar dai son Annbi (S.a.w) da kalamai masu kyau, wanda za a  faɗa mishi, sannan idan mun yi muna iya kaiwa kasuwar Ƙofar Wambai a lokacin mu bawa masu yin harkar sidika (CD) da wannan kaset. Lokacin ana yin kaset sai mu basu su, su za su cigaba da tallata mana abubuwanmu. Yanzu kuwa idan muka yi waƙoƙin siyasa muna shan wahala, domin sai mun nemo wanda muka yi wa, ko kuma ya karɓa, da dai sauransu. Shi ne dalilin da ya sa za ki ga a wannan lokacin akwai gwagwarmaya gaskiya, saboda dole idan ka yi wa wani kana buƙatar ya ji ko ya gani.

Ya batun iyaye lokacin da ki ka fara sanar musu kina so ki fara waƙa, shin kin fuskanci wani ƙalubale daga gare su?

Lokacin da nake so na faɗawa iyayena batun waƙa, ba kai tsaye na samu goyon baya daga gare su ba, saboda a lokacin sun zata irin waƙar fim ce, amma daga ƙarshe dai iyayennawa suka fahimci cewar yadda dai ƙaddara ta zo, suka yi min addu’a.

Ya farkon fara waƙar ya kasance?

Farkon fara waƙa ban sha wahala ba, saboda ni na rubuta waƙata da kaina, sannan kuma na je ‘studio’, akwai wani ‘studio’ a lokacin a nan Zoo Road gurinsu wata Hannatu Sakatariyya, gurinsu Tijjani Kazaure, a nan na fara aiki.

Da wanne mawaƙi ko mawaƙiya ki ka fara yin waƙa?

A lokacin da na fara waƙa ban taɓa yi da wani mawaƙi ba, saboda ni da kaina nake rubuta waƙa ta, amma a yanzu da yake an samu cigaba ni ma idan zan yi waƙa ina ɗaukar mace kamar, Allah ya ƙara mata lafiya Hajiya Zuwaira Isma’il ta na yi min amshi.

Kin yi waƙoƙi sun kai kamar guda nawa?

To, yanzu dai gaskiya ba zan iya tantance ko sun kai nawa ba, Allah ka ɗai ya sani.

Ko za ki iya faɗowa masu karatu sunayen kaɗan daga cikin waƙoƙin da ki ka rera ko ki ka rubuta?

Akwai waƙar da na yi a wancan lokacin ta ‘Annabi sai ɗangatau’, sai kuma ta Almajiri, akwai waƙa ta ‘Na shiga Soyayya’, sai waƙoƙin siyasa na APC. Sannan idan aka shiga ‘page’ ɗina mai suna ‘Fati Uk Jakadiya’ a Tiktok da Audiomack.

A cikin waƙoƙin da ki ka rera ko ki ka rubuta wacce waƙa ce ta zamo bakandamiyyarki?

A yanzu waƙar da ta zamo bakandamiyata, ita ce wacce na yi a kan Almajiri, kuma idan Allah ya so ya yarda ba zan daina sonta ba. Sannan ina fatan Al’umma su yi amfani da abubuwan da na ce a cikin waƙar, saboda waƙa ce na yi ta akan faɗakarwa akan harkar Almajiri.

Me ya fi baki wahala wajen rera waƙa ko rubutawa?

Abin da yafi ba ni wahala a wancan lokacin wajen waƙa, ko rera ta, saboda rubuta waƙa baya bani wahala, gurin hawa da sauka, shi ne ya fi ba ni wahala.

Wane irin nasarori ki ka samu game da waƙa?

Na samu nasarori, dalilin waƙa an naɗa min sarautu guda uku a kaina, an yi min alkyabbar Hausawan Africa, an yi min Jakadiyar Galadiman Kano, an yi min Gimbiyar Sha’iran ƙasar Hausa. Ta dalilin waƙa na yi ziyarce-ziyarcen garuruwa da ƙasashe, na yi aikin hajji na sauke farali, na yi umara babu adadi, na yi abubuwa da yawa, dalilin waƙar nan na yi kasuwanci na.

Ko kina da ubangida a ɓangaren waƙa?

A’a, ba ni da ubangida a ɓangaren waƙa, amma ina da abokanen mu’amala, abokanan sana’a, wanda kuma sun zama kamar yayyena, Alhamdulillah suna ba ni shawarwari masu kyau, amma ba ni da tsayayye kai tsaye wanda zan kira, misali in ce miki wai mawaƙi ne shi ubangida na, Allah shi ne wanda yake tsaya min.

Mene ne burinki na gaba game da waƙa ko kuma mawaƙa?

Buri na na gaba dangane da harkar nan da nake yi, ina fatan ubangiji Allah ya sa mutane su fahimci me ma nake yi, kin san akwai abin da kake yi wasu ma basu gane me kake yi ba. Fata na Allah Ubangiji ya sa mutane su fahinci me nake yi. Kuma ina fatan Allah ya sa abin da muke yi ya zama alkhairi a cikin Al’umma, sannan kuma mu gama lafiya, shi ne babban burina.

Wacce shawara za ki bawa masu ƙoƙarin fara waƙa?

Shawarar da zan bawa masu ƙoƙarin fara waƙa, su yi haƙuri su dage su yi juriya, harkar nan akwai wahala, dan idan ba ka da haƙuri gaskiya ba za ka samu duk nasarorin da kake son samu a ciki ba, amma idan suka yi haƙuri inda basa zato ma za su je. Sannan kuma idan sun tashi shigowa kada su shigo da niyyar za su yi kuɗi ko arziƙi, su jira Allah.

Ko kina da wata shawara da za ki bawa sauran mawaƙa?

Shawarata ga sauran mawaƙa ƴan’uwana, dan Allah don Annabi mu haɗa kanmu, mu daina munafurci, mu zama ƴan’uwa tsintsiya ɗaya maɗaurinki ɗaya, dan Allah mu cire hassada mu so junanmu, arziƙi Allah ne mai bayarwa.

Me za ki ce da masoyanki, masu sauraron waƙoƙinki?

Masu saurarona ina godiya, ina mana fatan alkhairi  gabaɗaya, sannan a cigaba da taya mu da addu’a, sannan idan kun ga wajen da muka yi kuskure ku sanar da mu ta inda ya dace, kuma ta inda zamu fahimce ku. Ina ƙara godiya ubangiji Allah ya bar zumuncinmu da ku, Allah kuma ya tabbatar mana da alkhairi bakiɗaya. Allah ya zaunar mana da ƙasar mu da ma duniyar mu bakiɗaya lafiya.

Ko kina da waɗanda za ki gaisar?

Ina gaida iyayen gidana na siyasa kamar Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ina gaishe da Distinguish Senator Barau Jibril Maliya. A cikin fim industry kuma ina gaishe da Hajiya Hauwa Editor da Daddy Hikima, da sauran jama’a musulmi. Allah ya sa mu gama lafiya.

Muna godiya ki huta lafiya.

Ni ma na gode, Allah ya saka da Alkhairi, Allah ubangiji ya bar zumunci, ya sa mu gama lafiya.

Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Hotunan Ango Da Amarya Kafin Daura Aure

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Bayan Harkar Fim, Sayar Da Abinci Ne Babbar Sana’ata – Aisha Yola
Nishadi

Bayan Harkar Fim, Sayar Da Abinci Ne Babbar Sana’ata – Aisha Yola

May 10, 2026
Next Post
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Nemi Tallafi Na Musamman Ga Alhazai Mata

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Nemi Tallafi Na Musamman Ga Alhazai Mata

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.