Uwargidan gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yi kira da a ba mata mahajjata cikakken kulawa da tallafi yayin da suke shirin tafiya ƙasa mai tsarki domin gudanar da aikin Hajji.
Ta kuma buƙaci dukkan mahajjatan da su kasance jakadu nagari na jihar da kuma Nijeriya baki ɗaya.
Wata sanarwa da Rabi Yusuf, sakatariyar yaɗa labarai ta Ofishin Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara da ke Gidan Gwamnatin Gusau ta sanya wa hannu, ta bayyana cewa kafin bikin yi wa mahajjatan bankwana, uwargidan gwamnan ta gudanar da wani muhimmin taro da shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Zamfara, Alhaji Musa Mallaha, da kuma ƙungiyar mata masu aikin sa kai ta hukumar.
“Domin nuna jajircewarta wajen kula da jin daɗin mata mahajjata, uwargidan gwamnan ta raba hijabai ga matan da za su gudanar da aikin Hajjin bana, domin tabbatar da cewa sun samu cikakken tallafi don wannan tafiya ta ibada.
“Taron ya mayar da hankali ne kan tsara hanyoyin gudanarwa domin tabbatar da jin daɗi da ingantacciyar kulawa ga mahajjatan, musamman mata.
“Tattaunawar ta shafi harkokin sufuri, walwala da muhimman ƙa’idojin gudanarwa domin tabbatar da tafiya mai sauƙi ba tare da wata matsala ba.”
Ta kuma shawarci mahajjatan da su rungumi halayen haƙuri, ladabi, haɗin kai da kyawawan ɗabi’u a duk lokacin da suke ƙasa mai tsarki.
Haka kuma ta ƙarfafa musu gwiwa da su yi amfani da wannan lokaci mai alfarma wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban Jihar Zamfara.
A nasa jawabin, shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Zamfara, Musa Mallaha, ya nuna godiya ga uwargidan gwamnan bisa ci gaba da tallafi da kulawar da take bai wa mahajjatan jihar.















Discussion about this post