ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kimar Mace Mara Sana’a Take A Wurin Mijinta?

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Mace

Duk sanda akace mutum yana da dan abun juyawa duk kankantar sa tabbas ya karawa kansa kima sannan ya ragewa kansa damuwa.Mace mau sana’a ko a wurin dangin miji kimarta daban take balle kuma akai ga shi kanshi mijin.To idan kuma uwargida ta maida kanta sai anci an bata to fa tabbas ta hadu da aikin jira dan kuwa duk yanda kike so kiyiwa kanki abu dole ki hakura sai an dauko an baki.

Kamar yadda aka sani uwargidan da batada kwakwarar sana’a adinga inda kaganta zaka tafita daban acikin tsara,kuma rashin dan na kashewa yana janyo abubuwa da Dama musamman a zamantakewar aure.

  • Kullum Tirela 200 Ce Za Su Riƙa Ɗaukar Mai A Matatar Fatakwal – Fadar Shugaban Ƙasa
  • Sin Ta Yi Tir Da Matakin Amurka Na Sayarwa Taiwan Makamai

Abu na farko mace mara sana’a zata kasance kullum cikin kunci bata san me ke mata dadi ba musamman ma idan mijin ba mai hali ba ne sosai,zata kasance ko zamantakewar ta da miji ma babu dadi kawai sai taji tana jin haushin shi batare da yayi mata wani kwakwaran laifi ba .

ADVERTISEMENT

Rashin sana’a na sa uwar gida ko acikin danginta ta zama mujiya ta koma kamar bare,sai abinda akaci aka bata ,ko shawara za ayi sai taga ana damawa kannenta masu dan abun hannun su amma ita kuwa ta zama bare.

Hakazalika rashin abin yi na sa uwargida ta zama ‘Depressed’ wato ta kasance cikin kuci ba tada walwala. Amma yau in uwargida zata samu dan abin juyawa zata kasance batada lokaci zama tayi tunanin banza ba lokacin ta zai kasance na juya taro ya koma sisi ne.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

Kamar yadda mawakiya Barmani Choge ta ke kirari a wakarta inda take cewa ‘a kama sana’a mata zaman banza ba namu ba’ to wannan magana haka take .Uwargida in kika kama sana’a ke kanki zakiji kin fi samun natsuwa yan kananan hidimar ki ba sai kin jira miji ya zo ya miki ba.Haka yara zaki taimakawa maigida da dan kanana hidimansu wanda dai baifi karfin ki ba, kuma ko su kansu yaran sun san ana musu in suna da dan bukatun su zakiga sun nufo ki amma ba wai in sunzo sun ce a basu kusin fensir ba ki ce to ku jira Baban ku ya dawo .Wannan yana rage daraja har a idon maigida.

Uwagidan da ta rike sana’a ko shi kanshi mijin yanda zai mata magana cikin fahimta daban ne da wacce take zaune zai an daga sai an tayar. In uwargida na juya biyar ta koma goma za taga yanayin zaman lafiya a gidan ma ya karu babu yawan gaba,babu yawan jin haushin juna ko kuma hantara.

Sana’a nasa miji ya kalle mace da daraja sa kuma kima saboda yawan bani bani ko a gidan ku ne yana jawo raini amma in kika kasance kina dan daukewa maigida wasu nauyi to fa duk duniya babu kamar ki.

Koda ace uwar gida tana hidima mijin baya nuna halin ko in kula yanuna kamar bai sani ba to fa cikin ransa ba karamin farin cikin yake yi ba dan yasan dole akwai kina dauke masa wasu tallafi.

Mata a gyara a rage zaman banza, a nemi sana’a akwai sana’o’i iri daban daban kala kala sai wanda kika zaba kamar su Dinki,turaren wuta, saida itace,saka,da dai sauran su kuma duk wanda uwar gida tasa kai zata iya kuma zata samu alheri sosai dan ta tallafawa kanta har ma da ‘yan uwanta.

Mace
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

MASU ALAKA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Ado Da Kwalliya

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Ado Da Kwalliya

Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

May 17, 2026
Next Post
Macen Da In Mijinta Ya Sadu Da Ita Maniyyi Ba Ya Zama

Macen Da In Mijinta Ya Sadu Da Ita Maniyyi Ba Ya Zama

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.