ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kimar Mace Mara Sana’a Take A Wurin Mijinta?

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Mace

Duk sanda akace mutum yana da dan abun juyawa duk kankantar sa tabbas ya karawa kansa kima sannan ya ragewa kansa damuwa.Mace mau sana’a ko a wurin dangin miji kimarta daban take balle kuma akai ga shi kanshi mijin.To idan kuma uwargida ta maida kanta sai anci an bata to fa tabbas ta hadu da aikin jira dan kuwa duk yanda kike so kiyiwa kanki abu dole ki hakura sai an dauko an baki.

Kamar yadda aka sani uwargidan da batada kwakwarar sana’a adinga inda kaganta zaka tafita daban acikin tsara,kuma rashin dan na kashewa yana janyo abubuwa da Dama musamman a zamantakewar aure.

  • Kullum Tirela 200 Ce Za Su Riƙa Ɗaukar Mai A Matatar Fatakwal – Fadar Shugaban Ƙasa
  • Sin Ta Yi Tir Da Matakin Amurka Na Sayarwa Taiwan Makamai

Abu na farko mace mara sana’a zata kasance kullum cikin kunci bata san me ke mata dadi ba musamman ma idan mijin ba mai hali ba ne sosai,zata kasance ko zamantakewar ta da miji ma babu dadi kawai sai taji tana jin haushin shi batare da yayi mata wani kwakwaran laifi ba .

ADVERTISEMENT

Rashin sana’a na sa uwar gida ko acikin danginta ta zama mujiya ta koma kamar bare,sai abinda akaci aka bata ,ko shawara za ayi sai taga ana damawa kannenta masu dan abun hannun su amma ita kuwa ta zama bare.

Hakazalika rashin abin yi na sa uwargida ta zama ‘Depressed’ wato ta kasance cikin kuci ba tada walwala. Amma yau in uwargida zata samu dan abin juyawa zata kasance batada lokaci zama tayi tunanin banza ba lokacin ta zai kasance na juya taro ya koma sisi ne.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

Kamar yadda mawakiya Barmani Choge ta ke kirari a wakarta inda take cewa ‘a kama sana’a mata zaman banza ba namu ba’ to wannan magana haka take .Uwargida in kika kama sana’a ke kanki zakiji kin fi samun natsuwa yan kananan hidimar ki ba sai kin jira miji ya zo ya miki ba.Haka yara zaki taimakawa maigida da dan kanana hidimansu wanda dai baifi karfin ki ba, kuma ko su kansu yaran sun san ana musu in suna da dan bukatun su zakiga sun nufo ki amma ba wai in sunzo sun ce a basu kusin fensir ba ki ce to ku jira Baban ku ya dawo .Wannan yana rage daraja har a idon maigida.

Uwagidan da ta rike sana’a ko shi kanshi mijin yanda zai mata magana cikin fahimta daban ne da wacce take zaune zai an daga sai an tayar. In uwargida na juya biyar ta koma goma za taga yanayin zaman lafiya a gidan ma ya karu babu yawan gaba,babu yawan jin haushin juna ko kuma hantara.

Sana’a nasa miji ya kalle mace da daraja sa kuma kima saboda yawan bani bani ko a gidan ku ne yana jawo raini amma in kika kasance kina dan daukewa maigida wasu nauyi to fa duk duniya babu kamar ki.

Koda ace uwar gida tana hidima mijin baya nuna halin ko in kula yanuna kamar bai sani ba to fa cikin ransa ba karamin farin cikin yake yi ba dan yasan dole akwai kina dauke masa wasu tallafi.

Mata a gyara a rage zaman banza, a nemi sana’a akwai sana’o’i iri daban daban kala kala sai wanda kika zaba kamar su Dinki,turaren wuta, saida itace,saka,da dai sauran su kuma duk wanda uwar gida tasa kai zata iya kuma zata samu alheri sosai dan ta tallafawa kanta har ma da ‘yan uwanta.

Mace
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Ado Da Kwalliya

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Ado Da Kwalliya

Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

May 17, 2026
Next Post
Macen Da In Mijinta Ya Sadu Da Ita Maniyyi Ba Ya Zama

Macen Da In Mijinta Ya Sadu Da Ita Maniyyi Ba Ya Zama

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.