Tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya na mulkin Soji, Yakubu Gowon, ya bayyana yadda wani amintaccen jami’in tsaronsa, Joseph Garba, wanda ya shugabanci rukunin masu tsaronsa, ya taka rawa wajen juyin mulkin da ya kifar da gwamnatinsa a watan Yulin 1975.
Gowon ya bayyana hakan ne a cikin littafinsa mai shafi 859 mai suna ‘My Life of Duty and Allegiance’, inda ya ce lamarin ya kasance ɗaya daga cikin manyan cin amana da ya taɓa fuskanta a rayuwarsa.
Ya ce mutanen da suka yi wannan abu su ne waɗanda ya amince da su kuma ya ɗaga su zuwa manyan muƙamai a cikin gwamnati da soji.
A cewarsa, Garba, wanda ke shugabantar rukunin tsaro na musamman da ke kare rayuwarsa, daga baya an gano yana da hannu shirin juyin mulkin.
Ya ce wannan ya fi masa zafi saboda Garba ya shaida masa kwanaki kaɗan kafin juyin mulkin cewa bai san komai game da wani shiri na kifar da gwamnati ba.
Gowon ya kuma bayyana cewa babban jami’in tsaronsa, M.D. Yusuf, ya riga ya yi masa gargaɗi cewa wasu jami’an soji na shirin yi masa juyin mulki kafin taron OAU a Kampala, Uganda.
Ya ambaci Joseph Garba da Anthony Ochefu a matsayin wasu daga cikin manyan waɗanda ake zargi.
Ya ce abin ya masa ciwo sosai saboda ya aminta da shi.
Ya ƙara da cewa ya naɗa Garba muhimmin matsayin tsaro ne saboda yadda yake da ƙwarin gwiwa a kansa.
Gowon ya ce wannan lamari ya kasance ɗaya daga cikin manyan abubuwan da suka fi masa ciwo a rayuwarsa, ganin cewa waɗanda suka yi abin su ne mutanen da ya yi matuƙar aminta da su.















Discussion about this post