Tsohon gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong, tare da wasu ‘yan siyasa sun lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC domin takarar kujerun Majalisar Dokoki ta Ƙasa da aka gudanar a faɗin jihar.
Lalong ya samu tikitin takarar Sanatan Filato ta Kudu bayan da ya fi kowa yawan ƙuri’u.
A Filato ta Arewa kuwa, Simon Mwadkwon ya lashe tikitin Sanata da gagarumin rinjaye, yayin da ɗan kasuwa David Bitrus Barji ya kayar da Sanata Diket Plang da sauran ‘yan takara domin samun tikitin Filato ta Tsakiya.
A zaɓen kujerun Majalisar Wakilai kuwa, Beni Lar ta lashe tikitin Langtang ta Arewa da Langtang ta Kudu, yayin da Musa Bagos ya yi nasara a Jos ta Kudu da Jos ta Gabas.Haka kuma kwamitin ya bayyana Yusuf Gagdi a matsayin wanda ya lashe tikitin Pankshin/Kanam/Kanke.
Sauran waɗanda suka yi nasara sun haɗa da Hon. Joshua Dashe na Qua’an Pan/Mikang/Shendam, Hon. Idris Maje Wase wanda zai wakilci mazaɓar Wase, da Amb. Abubakar Sadiq Plaza na Jos ta Arewa/Bassa.
Da take sanar da sakamakon a Jos, shugabar Kwamitin Zaɓen Fidda Gwani na APC a Filato, Stella Okotete, ta bayyana zaɓen a matsayin wanda aka gudanar cikin lumana, gaskiya da adalci.
Ta yaba wa shugabannin APC, gwamnan Jihar Filato Caleb Mutfwang, masu ruwa da tsaki da kuma ‘ya’yan jam’iyya bisa tabbatar da zaman lafiya yayin gudanar da zaɓen.















Discussion about this post