• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Tarbiya Ke Haifar Da Jinkirin Auren ‘Yan Mata A Wannan Zamanin

by Rabi'at Sidi Bala
7 months ago
in Taskira
0
Yadda Rashin Tarbiya Ke Haifar Da Jinkirin Auren ‘Yan Mata A Wannan Zamanin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yadda Rashin Tarbiyya ‘Ya’ya Mata Ke Sanadiyar Jinkirin Aurensu, Ko Me Zakuce A Kan Hakan? Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacimmu na yau zai yi duba ne game da jinkirin auren ‘ya’ya mata a wannan zamanin.

  • Yawan Karuwar GDPn Sin Daga Watan Janairu Zuwa Satumban Bana Ya Kai 4.8% Bisa Na Makamancin Lokacin A Bara
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Bilkisu Maharazu

Assalamu alaikum. Agaskiya matsalolin da ake samu dangane da rashin tarbiyya da yake shafar ‘ya’ya mata sun hada da rashin kwabar su tun suna kanana domin shi ice tun yana danye ake tankwara shi in ya bushe ba ya tankwaruwa, yana da kyau tun yarinya tana karama a bata tarbiyya mai kyau yadda idan ta girma za ta tashi da ita ba tare da an samu tangarda ba, domin ‘yan magana suna cewa tarbiyya daga gida take faraway. Wasu mazaje suna lura da tarbiyyar mace kafin su aure ta kamar yadda shari’a ta ce ka nema wa ‘ya’anka uwa ta gari, Allah ya sa mu dace.

Rukayya Habibu

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

Hakika lamarin rashin tarbiyya ba karamin cikas yake kawo ba musamman ma idan maganar neman aure ta taso, wannan lamarin ba wai ya tsaya ne akan ‘ya’ya mata ba har ma maza, duk da yake dai abin ya fin illa ga su ’ya’ya mata saboda duk dadewa da za su yi wata rana sai sun samu masu aurensu.

Duk da yake dai daga karshe su ‘ya’ya mata aurensu za a yi, kowace kuma yadda halinta yake zai nuna irin yadda lamarin zaman aure zai kasance. Ko ba magana lalle kowa ya san tarbiyya tagari na jawo hankali musamman ma a ce a gida iyaye sun taka muhimmiyar rawa wajen ba da gudunmawa dangane da tarbiyya, saboda sanin kowa ne ice tun yana karami ake tankwara shi, in ya riga ya girma kuma, abin za iyi wuya manufa ana iya haduwa da matsala.

Malam Dauda Argungu mazaunin Mararraba

Ai dama duk inda ruwa ya je ya dawo kwari zai zauna, irin dabi’un Iyyaye suna taka rawa wajen yadda tarbiyyar ‘ya’yansu take kasancewa, saboda su duk abin da ‘ya’ya suka gani daga wurin iyayensu abin da tunaninsu zai basu ai masu kyau ne, don haka za su yi kokarin yin koyi da su. Shi ya sa akwai bukatar sa ido wajen lura da yadda tarbiyyar ‘ya’ya take ba ma kamar mata su komai dadewa gidan wani ne za su je.

Wasu ‘ya’yan ba laifinsu bane domin ai ana ganinsu saboda zama tare da su, da zarar an ga suna neman kauce hanya sai a maido su wadda ya dace su bi.

Habiba Tijjani

A gaskiya rashin tarbiyyar ba karamar taka rawa yake ba wajen sanadiyyar aure saboda za ki ga koda tafiya ta yi nisa tsakanin ma’aurata wato sun shaku da junansu musamman ma idan aka ce saurayi da budurwa ne to idan ya kai maganar gidansu abin da za’a fara tambayarsa shi ne ya tarbiyyar ta ta take ka binciki tarbiyyarta idan ya amsa musu to fa ba za su tsaya ga maganarsa ba sai suma sun yi nasu binciken iya bincike, sannan binciken da za su yi ba wai iya yarinyar kadai ba a’a babban abin da za su fara bincike a kai shi ne, da farko gidansu ya iyayenta su suma ya tarbiyyar su take, to daga nan ne za a iya kano iyayen suna da cikakkiyar tarbiyyar da har za su iya auren diyarsu?

Sai kuma a koma kan ita yarimyar, shin tarbiyyar da iyayenta suka ba ta tana amfani da ita ko kuma idan ta fita tana daukar wadansu daban, nan ma sai a yi bincike ya mu’amalarta take a waje, yarinya ce mai mutunci, mai da’a da sanin darajar mutane, shin ta iya girmama mutane, ta san girman na gaba da ita? Duk wannan sai an san su da zarar an samu akasin daya daga cikin wadannan sai ki ga amfara samun matsaloli ana bashi shawara idan kuma shima gidansu tsayayyu, ne sai ki ji suna cewa wannan auran ba zai yiyu ba ya canja wata to kin ga rashin tarbiyyar gaskiya ba karamar illa bace ga rayuwar ‘ya mace. Allah ya sa mu dace.

Usman Sani

Gaskiya yanzu lalacewa tarbiyyar ya tabarbare a wannan zamani wasu rashin tarbiyya tana farawa ne run daga gida, kuma ba wai iyayen ne ba su da tarbiyya ba a’a sun yaran ne yake kawo iyayen ba sa iya ba su kyakkyawar tarbiyya, saboda suna gudun bacin ran yaran shi ya sa iyayen ba za su iya dora su akan turba mai kyau ba sai dai a shagwaba su to kin ga ba kowanne namiji ne zai dauki komai ba za ki ga iyaye suna da tarbiyyar amma yaran sai yadda suke so haka za a yi.

To a gaskiya ya kamata mu rage nuna wa yara so da yawa saboda ya bamu damar nuna musu turbar da take daidai da wadda ba daidai ba mu kuma hada da addu’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureTarbiyyaTasiri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gurasa Na Zamani

Next Post

Masu Sha’awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa

Related

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu
Taskira

Yadda Wasu Mata Ke Gallaza Wa ‘Ya’yansu Domin Bakanta Wa Mazajensu

2 weeks ago
Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
Taskira

Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?

4 weeks ago
Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma
Taskira

Yadda Rashin Ilimi Ke Cutar Da Rayuwar Al’umma

1 month ago
Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?
Taskira

Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?

2 months ago
Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Yaran Ba Sa Jin Maganar Iyayensu?

4 months ago
Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?
Taskira

Me Ke Sa Mata Gallaza Wa Yaran Da Aka Bar Musu Amana?

4 months ago
Next Post
Masu Sha’awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa

Masu Sha'awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.