ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rashin Tarbiya Ke Haifar Da Jinkirin Auren ‘Yan Mata A Wannan Zamanin

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
Aure

Yadda Rashin Tarbiyya ‘Ya’ya Mata Ke Sanadiyar Jinkirin Aurensu, Ko Me Zakuce A Kan Hakan? Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma.

Tsokacimmu na yau zai yi duba ne game da jinkirin auren ‘ya’ya mata a wannan zamanin.

  • Yawan Karuwar GDPn Sin Daga Watan Janairu Zuwa Satumban Bana Ya Kai 4.8% Bisa Na Makamancin Lokacin A Bara
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Bilkisu Maharazu

ADVERTISEMENT

Assalamu alaikum. Agaskiya matsalolin da ake samu dangane da rashin tarbiyya da yake shafar ‘ya’ya mata sun hada da rashin kwabar su tun suna kanana domin shi ice tun yana danye ake tankwara shi in ya bushe ba ya tankwaruwa, yana da kyau tun yarinya tana karama a bata tarbiyya mai kyau yadda idan ta girma za ta tashi da ita ba tare da an samu tangarda ba, domin ‘yan magana suna cewa tarbiyya daga gida take faraway. Wasu mazaje suna lura da tarbiyyar mace kafin su aure ta kamar yadda shari’a ta ce ka nema wa ‘ya’anka uwa ta gari, Allah ya sa mu dace.

Rukayya Habibu

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Hakika lamarin rashin tarbiyya ba karamin cikas yake kawo ba musamman ma idan maganar neman aure ta taso, wannan lamarin ba wai ya tsaya ne akan ‘ya’ya mata ba har ma maza, duk da yake dai abin ya fin illa ga su ’ya’ya mata saboda duk dadewa da za su yi wata rana sai sun samu masu aurensu.

Duk da yake dai daga karshe su ‘ya’ya mata aurensu za a yi, kowace kuma yadda halinta yake zai nuna irin yadda lamarin zaman aure zai kasance. Ko ba magana lalle kowa ya san tarbiyya tagari na jawo hankali musamman ma a ce a gida iyaye sun taka muhimmiyar rawa wajen ba da gudunmawa dangane da tarbiyya, saboda sanin kowa ne ice tun yana karami ake tankwara shi, in ya riga ya girma kuma, abin za iyi wuya manufa ana iya haduwa da matsala.

Malam Dauda Argungu mazaunin Mararraba

Ai dama duk inda ruwa ya je ya dawo kwari zai zauna, irin dabi’un Iyyaye suna taka rawa wajen yadda tarbiyyar ‘ya’yansu take kasancewa, saboda su duk abin da ‘ya’ya suka gani daga wurin iyayensu abin da tunaninsu zai basu ai masu kyau ne, don haka za su yi kokarin yin koyi da su. Shi ya sa akwai bukatar sa ido wajen lura da yadda tarbiyyar ‘ya’ya take ba ma kamar mata su komai dadewa gidan wani ne za su je.

Wasu ‘ya’yan ba laifinsu bane domin ai ana ganinsu saboda zama tare da su, da zarar an ga suna neman kauce hanya sai a maido su wadda ya dace su bi.

Habiba Tijjani

A gaskiya rashin tarbiyyar ba karamar taka rawa yake ba wajen sanadiyyar aure saboda za ki ga koda tafiya ta yi nisa tsakanin ma’aurata wato sun shaku da junansu musamman ma idan aka ce saurayi da budurwa ne to idan ya kai maganar gidansu abin da za’a fara tambayarsa shi ne ya tarbiyyar ta ta take ka binciki tarbiyyarta idan ya amsa musu to fa ba za su tsaya ga maganarsa ba sai suma sun yi nasu binciken iya bincike, sannan binciken da za su yi ba wai iya yarinyar kadai ba a’a babban abin da za su fara bincike a kai shi ne, da farko gidansu ya iyayenta su suma ya tarbiyyar su take, to daga nan ne za a iya kano iyayen suna da cikakkiyar tarbiyyar da har za su iya auren diyarsu?

Sai kuma a koma kan ita yarimyar, shin tarbiyyar da iyayenta suka ba ta tana amfani da ita ko kuma idan ta fita tana daukar wadansu daban, nan ma sai a yi bincike ya mu’amalarta take a waje, yarinya ce mai mutunci, mai da’a da sanin darajar mutane, shin ta iya girmama mutane, ta san girman na gaba da ita? Duk wannan sai an san su da zarar an samu akasin daya daga cikin wadannan sai ki ga amfara samun matsaloli ana bashi shawara idan kuma shima gidansu tsayayyu, ne sai ki ji suna cewa wannan auran ba zai yiyu ba ya canja wata to kin ga rashin tarbiyyar gaskiya ba karamar illa bace ga rayuwar ‘ya mace. Allah ya sa mu dace.

Usman Sani

Gaskiya yanzu lalacewa tarbiyyar ya tabarbare a wannan zamani wasu rashin tarbiyya tana farawa ne run daga gida, kuma ba wai iyayen ne ba su da tarbiyya ba a’a sun yaran ne yake kawo iyayen ba sa iya ba su kyakkyawar tarbiyya, saboda suna gudun bacin ran yaran shi ya sa iyayen ba za su iya dora su akan turba mai kyau ba sai dai a shagwaba su to kin ga ba kowanne namiji ne zai dauki komai ba za ki ga iyaye suna da tarbiyyar amma yaran sai yadda suke so haka za a yi.

To a gaskiya ya kamata mu rage nuna wa yara so da yawa saboda ya bamu damar nuna musu turbar da take daidai da wadda ba daidai ba mu kuma hada da addu’a.

Aure
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Taskira

Ra’ayin Al’umma Game Da Shirin Gwamnati Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 11, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?
Taskira

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
Taskira

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Next Post
Masu Sha’awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa

Masu Sha'awar Shiga Harkar Fim Su Shiga Da Zuciya Daya -Auwal Marafa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.